ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Zamfara Na Da Rinjaye A Fannin Noma, In Ji Gwamna Lawal A Taron AIF Na Morocco

by Sulaiman
6 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sake jaddada wa duniya cewa Jihar Zamfara na da babbar damar bunƙasa harkokin noma, yana mai cewa noma ne ginshiƙin ci gaban tattalin arzikin jihar da Arewa maso Yamma gaba ɗaya.

 

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Mai Magana da Yawun Gwamnan Jihar Zamfara Sulaiman Bala Idris ya fitar a ranar 29 ga watan Nuwamba, inda ya ce, Gwamna Lawal ya yi wannan bayani ne yayin da ya halarci Babban Taron Masu Zuba Jari na Afirka (AIF), Ranakun Kasuwar Zuba Jari na 2025 da aka gudanar daga ranakun 26 zuwa 28 ga watan Nuwamba, 2025, a birnin Rabat da ke ƙasar Morocco.

ADVERTISEMENT
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Inganta Hanyoyin Kula Da Tafiyar Da Intanet Na Dogon Zango
  • Hong Kong Ta Yi Jimamin Wadanda Gobara Ta Shafa Ta Hanyar Saukar Da Tutoci

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce taron ya haɗa manyan masu zuba jari daga sassa daban-daban na Afirka, inda aka tattauna manyan yarjejeniyoyin kasuwanci tare da lalabo hanyoyin aiwatar da ainihin zuba jari a faɗin nahiyar.

 

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Sanarwar ta ce, taron, wanda Bankin Raya Afirka tare da haɗin gwiwar wasu manyan cibiyoyi guda shida ke jagoranta, ya mayar da Taron Zuba Jari na Afrika a matsayin dandali na musamman da ke hanzarta tsara manyan ayyukan ci gaba da tara kuɗaɗen da za su tafiyar da su a Afirka.

Zamfara

A yayin taron, Gwamna Lawal ya halarci manyan tattaunawa kan yadda za a bunƙasa zuba jarin kamfanoni masu zaman kansu ta hanyar samar da yanayi mai sauƙi, da kuma zaman muhawara kan faɗaɗa zuba jari ta tsarin haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu, tare da tattaunawa kan yadda za a tara jarin cikin gida domin ingiza ci gaban Afirka.

 

A gefe guda kuma, Gwamnan ya rattaba hannu kan wata muhimmiya Yarjejeniyar Fahimtar Juna tsakanin Gwamnatin Jihar Zamfara da Hukumar ‘Ministry of Finance Incorporated’ (MOFI) domin haɓaka gagarumin shirin sauya fasalin noma a jihar.

 

Yarjejeniyar ta sanya Zamfara a cikin jihohin da za su fi cin gajiyar shirin INTEGRANIUM na ƙasa, wanda ke mai da hankali kan noma na zamani, sarrafa amfanin gona, hanyoyin adana bayan girbi da kuma buɗe hanyoyin fitar da kayayyaki zuwa kasuwannin duniya.

 

A ƙarƙashin yarjejeniyar, Gwamnatin Jihar Zamfara za ta samar da filaye, ababen more rayuwa, tsaro da manufofi masu sauƙi, yayin da MOFI za ta jagoranci samo kuɗaɗen zuba jari, jawo hankalin masu zuba jari, da tallafa wa aiwatar da manyan ayyukan noma.

 

Ana sa ran wannan haɗin gwiwar zai samar da dubban ayyukan yi, ya ƙara wadatar abinci, ya ƙarfafa darajar amfanin gona tare da hanzarta ci gaban tattalin arziki mai shafar talakawa a Zamfara da yankin Arewa maso Yamma gaba ɗaya.

 

Da yake jawabi ga masu zuba jari a wani zagayen tattaunawa, Gwamna Lawal ya bayyana Zamfara a matsayin cibiyar noma ta haƙiƙa, yana mai cewa gwamnatinsa na samun gagarumar nasara a fannoni daban-daban.

Zamfara

A cewarsa, “Ina matuƙar farin ciki da ganin Bankin Raya Afirka tare da sauran manyan masu zuba jari na duniya sun halarci wannan taro. Noma ne gaba ga Afirka, Nijeriya da kuma Zamfara musamman, saboda yalwar damar da ake da ita. A Zamfara, noma shi ne rinjayenmu. Muna noman kusan dukkan nau’o’in amfanin gona; ba mu tsaya kan wake ko waken soya kaɗai ba. Muna da yalwatacciyar ƙasa mai albarka.

 

“Ina gayyatar dukkan masu zuba jari na duniya su zo Zamfara. A halin yanzu muna matakin ƙarshe na kammala filin jirgin saman ƙasa da ƙasa na jigilar kaya, muna gina otel mai matsayi na biyar, tare da manyan ayyukan sabunta birane a faɗin jihar.”

 

Gwamnan ya jaddada cewa gwamnatinsa na ɗora babban alheri kan noma a matsayin ginshiƙin wanzar da ayyukan yi ga matasa, rage talauci da tabbatar da tsaron abinci mai ɗorewa a Zamfara.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Shugabar Kasar Iceland:Taron Koli Na Mata Na Duniya Na Da Matukar Ma’ana Ga Kasashe Daban Daban

Shugabar Kasar Iceland:Taron Koli Na Mata Na Duniya Na Da Matukar Ma’ana Ga Kasashe Daban Daban

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.