ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, September 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jonathan Ya Buƙaci A Ƙarawa Ma’aikata Albashi

by Abubakar Sulaiman
56 minutes ago

Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da gwamnatocin jihohi su duba yiwuwar ƙarin albashin ma’aikata, domin ma’aikatan da ke gudanar da ayyuka iri ɗaya su riƙa samun albashi da matsayi makamancin juna. Ya bayyana hakan ne a Yenagoa, babban birnin Jihar Bayelsa, ranar Juma’a, 18 ga Satumba, 2026.

Jonathan ya yi wannan kira ne a wajen bikin aza harsashin ginin sakatariyar Ƙungiyar Tsofaffin Sakatarorin Gwamnatin Bayelsa. Ya ce bai kamata daraktan da ke aiki a gwamnatin jiha ya kasance a mataki na 16, alhali takwaransa a Gwamnatin Tarayya yana mataki na 17 ba, idan suna da cancanta da nauyin aiki iri ɗaya.

Tsohon shugaban ƙasar ya tuna cewa lokacin da yake gwamnan Bayelsa, ya sake fasalin ma’aikatan jihar, inda ya samar da mataki na 17 ga daraktoci waɗanda a baya suke ritaya a mataki na 16. Ya ce ya umarci Sakataren Gwamnati, Shugaban Ma’aikata da Akanta Janar na jihar da su aiwatar da sauyin, domin daidaita matsayin daraktocin jihar da takwarorinsu na tarayya. Ya kuma yi misali da malaman jami’o’i, yana mai cewa farfesan da ke koyarwa a jami’ar tarayya ya kamata ya samu albashi irin na takwaransa a jami’ar jiha.

ADVERTISEMENT

A nasa jawabin, Gwamnan Bayelsa, Douye Diri, wanda Shugaban Ma’aikatan jihar, Dakta Ebiye Sawyer, ya wakilta, ya yi alƙawarin cewa gwamnati za ta tallafa wajen kammala aikin sakatariyar. Shugaban ƙungiyar, King Collins Ebi Daniel, ya ce ginin zai ƙunshi ofisoshi, da ɗakunan taro da wuraren nishaɗi, kuma ana sa ran zai ci Naira miliyan 500 tare da kammala shi cikin shekaru biyu.

Jonathan ya yaba wa tsofaffin sakatarorin gwamnatin bisa yunƙurinsu na gina cibiyar da zai amfani mambobin ƙungiyar da sauran al’umma. Wasu mahalarta taron sun kuma ba da shawarar mayar da cibiyar wata cibiyar nazarin manufofi da za ta taimaka wajen bunƙasa jihar da ƙasa baki ɗaya.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Kwamandojin Ƴan Ta’adda A Katsina

Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Kama Kwamandojin Ƴan Ta’adda A Katsina
  • Abubakar Sulaiman
    Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro
  • Abubakar Sulaiman
    Tinubu Ya Janye Shirin Halartar UNGA, Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 9 A Sabbin Hare-Hare A Filato

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Kwamandojin Ƴan Ta’adda A Katsina
Labarai

Sojoji Sun Kama Kwamandojin Ƴan Ta’adda A Katsina

September 20, 2026
Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro
Labarai

Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro

September 20, 2026
Kano Pillars Ta Lallasa Doma United Da Ci 4-1 A Sani Abacha
Labarai

Kano Pillars Ta Lallasa Doma United Da Ci 4-1 A Sani Abacha

September 20, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kama Kwamandojin Ƴan Ta’adda A Katsina

Sojoji Sun Kama Kwamandojin Ƴan Ta’adda A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Kwamandojin Ƴan Ta’adda A Katsina

Sojoji Sun Kama Kwamandojin Ƴan Ta’adda A Katsina

September 20, 2026
Jonathan Ya Buƙaci A Ƙarawa Ma’aikata Albashi

Jonathan Ya Buƙaci A Ƙarawa Ma’aikata Albashi

September 20, 2026
Tawagar Kasar Sin Ta Lashe Lambobin Zinare 11 A Ranar Farko Ta Gasar Wasanni Ta Asiya

Tawagar Kasar Sin Ta Lashe Lambobin Zinare 11 A Ranar Farko Ta Gasar Wasanni Ta Asiya

September 20, 2026
Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro

Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro

September 20, 2026
Sin Ta Harba Tauraron Dan’adam Na Gwaji Da Ya Hade Ayyukan Sadarwa Da Tattara Bayanai Da Sarrafa Su

Sin Ta Harba Tauraron Dan’adam Na Gwaji Da Ya Hade Ayyukan Sadarwa Da Tattara Bayanai Da Sarrafa Su

September 20, 2026
Kano Pillars Ta Lallasa Doma United Da Ci 4-1 A Sani Abacha

Kano Pillars Ta Lallasa Doma United Da Ci 4-1 A Sani Abacha

September 20, 2026
Osimhen Ba Zai Buga Wa Nijeriya Wasannin Madagascar Da Guinea-Bissau Ba

Osimhen Ba Zai Buga Wa Nijeriya Wasannin Madagascar Da Guinea-Bissau Ba

September 20, 2026
An Bude Taron Masana’antun Kere-Kere Na Duniya Na Shekarar 2026 A Hefei Na Lardin Anhui

An Bude Taron Masana’antun Kere-Kere Na Duniya Na Shekarar 2026 A Hefei Na Lardin Anhui

September 20, 2026
Tinubu Ya Janye Shirin Halartar UNGA, Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya

Tinubu Ya Janye Shirin Halartar UNGA, Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya

September 20, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 9 A Sabbin Hare-Hare A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 9 A Sabbin Hare-Hare A Filato

September 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.