Alhaji Ibrahim Idris, wanda aka fi sani da Ibro, ya jagoranci Jihar Kogi daga 2003 zuwa 2012 a ƙarƙashin jam’iyyar PDP. A tsawon kusan shekaru tara da ya yi kan karagar mulki, gwamnatinsa ta aiwatar da ayyuka a fannoni daban-daban, musamman ilimi, da lafiya da samar da ababen more rayuwa.
Ga manyan ayyuka bakwai da ake dangantawa da gwamnatinsa.
1. Gina Asibitin Kwararru A Lokoja: Gwamnatinsa ta gina babban asibitin ƙwararru mai gadaje 400 a Lokoja, domin faɗaɗa damar samun ingantaccen kiwon lafiya a jihar.
2. Gina Makarantu A Faɗin Jihar: An gina kusan azuzuwa 2,000 na makarantun firamare, domin ƙara wa yara damar samun ilimi.
3. Bunƙasa Jami’ar Jihar Kogi: Gwamnatinsa ta tallafa wa Jami’ar Jihar Kogi da ke Anyigba, inda aka samu cikakken amincewa ga kwasa-kwasan karatunta guda 29 cikin watanni 29, a cewar wani rahoton The Nation na 2018.
4. Gina Filin Wasan Confluence: Filin wasan Confluence da ke Lokoja na daga cikin muhimman ayyukan more rayuwa da ake dangantawa da gwamnatinsa, domin bunƙasa wasanni a jihar.
5. Gina Kasuwar Ƙasa Da Ƙasa: Kasuwar International Market da ke Lokoja na daga cikin manyan ayyukan kasuwanci da gwamnatinsa ta aiwatar, da nufin inganta harkokin cinikayya.
6. Samar Da Gidaje Ga Ma’aikata: Gwamnatinsa ta gina gidajen ma’aikata a Lokoja da sauran ƙananan hukumomin jihar, a wani yunƙuri na samar da matsuguni ga ma’aikatan gwamnati.
7. Inganta Hanyoyi Da Samar Da Ruwa: Ayyukan gwamnatinsa sun haɗa da faɗaɗa manyan hanyoyin Lokoja da kuma shirin samar da ruwan sha na Greater Lokoja Water Scheme.
Waɗannan ayyuka na daga cikin abubuwan da ake dangantawa da tarihin mulkin Ibrahim Idris a Kogi.













