ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, September 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 9 A Sabbin Hare-Hare A Filato

by Abubakar Sulaiman
53 minutes ago

Aƙalla mutane tara ne suka mutu a wasu hare-haren ƴan bindiga da aka kai a yankunan Barkin Ladi da Riyom, da wasu al’ummomin da ke maƙwabtaka da su a Jihar Filato, tsakanin daren Asabar da safiyar Lahadi, 20 ga Satumba, 2026.

Daga cikin waɗanda aka kashe akwai fasinjoji da ke kan hanyarsu ta zuwa Gana-Ropp da kuma wani fasto da ke hanyar zuwa coci.

Rahotanni sun ce mutane biyar ne aka kashe a Gana-Ropp da ke Ƙaramar Hukumar Barkin Ladi, bayan wasu mahara sun farmaki fasinjojin da ke tafiya a matsayin ma’aikata. Shugaban Ƙungiyar Ci gaban Mwaghavul (MDA), Bulus Dabit, ya tabbatar da kisan, yayin da shugaban matasan Pyem na Gana-Ropp, Ukasha Garaba, ya ce an kwashe gawarwakin mutum biyar daga wurin harin.

ADVERTISEMENT

A wani harin daban da aka kai a Dorowa Babuje, Barkin Ladi, an kashe mutane biyu, ciki har da wani fasto, waɗanda ke kan hanyarsu ta zuwa coci a safiyar Lahadi. Haka kuma, an kashe wata mata a Baten Wereng, Ƙaramar Hukumar Riyom, a daren Asabar, 19 ga Satumba, yayin da aka kashe wani mutum a Ratyidi, da ke gundumar Fan.

Mai magana da yawun Ƙungiyar Berom Youth Moulders (BYM), Rwang Tengwong, ya tabbatar da hare-haren tare da yin Allah-wadai da kashe-kashen. Ya buƙaci jami’an tsaro su ƙara yawan jami’ai a yankunan da ke cikin haɗari domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a. A halin da ake ciki kuma, an rawaito satar wasu shanu a Dorowa Maranba da yankin Kantoma da misalin ƙarfe 3 na dare, inda sakataren MACBAN na Barkin Ladi, Gambo Abubakar, ya tabbatar da rahoton satar tare da kira ga jami’an tsaro su gudanar da bincike.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Ce A Shirye Yake Ya Sasanta Gwamna Yusuf

NSCDC Ta Kama Mutane Biyar Kan Zargin Sayar Da Naman Mushen Shanu A Yobe

Bulus Dabit ya yi kira ga hukumomi da su ƙarfafa tsaro a yankunan da hare-hare suka fi shafa, domin bai wa mazauna damar gudanar da harkokinsu cikin kwanciyar hankali. Ya ce hare-haren da ake ci gaba da kai wa na jefa al’umma cikin tsoro da fargaba, yana mai buƙatar a kamo waɗanda suka aikata laifukan tare da gurfanar da su a gaban shari’a.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Ƴan Bindiga Suka Kashe Ƴan Kasuwa 3 A Filato
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 12, Sun Ceto Mutane 66 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
  • Abubakar Sulaiman
    An Dakatar Da Jami’an NSCDC 21 Kan Mutuwar Masu Haƙar Ma’adinai A Neja
  • Abubakar Sulaiman
    Ku Rage Farashin Mai, Ku Sakarwa Ƴan Nijeriya Mara – Atiku Ga Tinubu

MASU ALAKA

Kwankwaso Ya Ce A Shirye Yake Ya Sasanta Gwamna Yusuf
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Ce A Shirye Yake Ya Sasanta Gwamna Yusuf

September 20, 2026
NSCDC Ta Kama Mutane Biyar Kan Zargin Sayar Da Naman Mushen Shanu A Yobe
Labarai

NSCDC Ta Kama Mutane Biyar Kan Zargin Sayar Da Naman Mushen Shanu A Yobe

September 20, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Radda Ya Ƙaddamar Da Shirin Tsaron Abinci Da Tallafawa Matasa A Katsina

September 20, 2026

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 9 A Sabbin Hare-Hare A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 9 A Sabbin Hare-Hare A Filato

September 20, 2026
Kwankwaso Ya Ce A Shirye Yake Ya Sasanta Gwamna Yusuf

Kwankwaso Ya Ce A Shirye Yake Ya Sasanta Gwamna Yusuf

September 20, 2026
NSCDC Ta Kama Mutane Biyar Kan Zargin Sayar Da Naman Mushen Shanu A Yobe

NSCDC Ta Kama Mutane Biyar Kan Zargin Sayar Da Naman Mushen Shanu A Yobe

September 20, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Radda Ya Ƙaddamar Da Shirin Tsaron Abinci Da Tallafawa Matasa A Katsina

September 20, 2026
Pate Ya Jinjina Wa Sauye-sauye Da Inganta Harkokin Lafiya A Katsina

Pate Ya Jinjina Wa Sauye-sauye Da Inganta Harkokin Lafiya A Katsina

September 20, 2026
An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Na Hanyar Siliki Karo Na 13 A Xi’an

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Na Hanyar Siliki Karo Na 13 A Xi’an

September 20, 2026
Ko Kano Pillars Za Su Iya Taka Wa Doma United Burki A Yau?

Ko Kano Pillars Za Su Iya Taka Wa Doma United Burki A Yau?

September 20, 2026
An Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Asiya Karo Na 20 A Nagoya Na Japan

An Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Asiya Karo Na 20 A Nagoya Na Japan

September 20, 2026
Trump Ya Hana CNN Da Wasu Kafofin Yaɗa Labarai Shiga Fadar White House

Trump Ya Hana CNN Da Wasu Kafofin Yaɗa Labarai Shiga Fadar White House

September 19, 2026
Adadin Tafiye-Tafiyen Da Jiragen Kasa Masu Jigilar Fasinjoji Suka Yi A Sin Ya Kai Matsayin Koli A Watanni 8 Na Bana

Adadin Tafiye-Tafiyen Da Jiragen Kasa Masu Jigilar Fasinjoji Suka Yi A Sin Ya Kai Matsayin Koli A Watanni 8 Na Bana

September 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.