Yau Laraba 20 ga wannan wata, kakakin ofishin kula da harkokin yankin Taiwan na majalisar gudanarwar kasar Sin Chen Binhua, ya yi tsokaci game da jawabin jagoran yankin Taiwan na ranar 20 ga watan Mayu, tare da amsa tambayoyin ‘yan jarida game da batun, inda ya yi nuni da cewa, jawabin jagoran yankin Taiwan Lai Ching-te na wannan rana na cike da jita-jita da ra’ayin nuna kiyayya, kasancewarsa mai bin tafarkin ‘yan aware da haddasa batun cewa babban yankin kasar Sin yana kawo barazana ga yankin, da sa kaimi ga nuna kiyayya a tsakanin gabobi biyu na mashigin tekun Taiwan, da kuma kawo illa ga zaman lafiya a tsakanin babban yankin kasar Sin da yankin Taiwan.
Chen Binhua ya kara da cewa, yankin Taiwan yanki ne na kasar Sin, shi ba wata kasa ba ce tun daga wancan lokacin har ma da nan gaba. Tabbatar da ‘yancin ikon mallakar kasar Sin da kiyaye martabar yankunanta shi ne tunanin dukkan jama’ar kasar Sin baki daya. (Zainab Zhang)















Discussion about this post