ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Da Wasu Jiga-jigan APC Sun Samu Tikitin APC Ta Hanyar Sulhu

by Shehu Yahaya and Sulaiman
3 weeks ago
APC

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Dahiru Liman; da Mataimakin Shugaban Majalisar, Magaji Henry Danjuma, tare da shugabar Masu Rinjaye ta Majalisar, Munira Suleiman Tanimu, sun zama ‘yan takarar Jamiyyar (APC) domin wakiltar mazabunsu bayan gudanar da tantancewar sulhu a sassa daban-daban na jihar.

An tabbatar da Hon. Dahiru Liman a matsayin ɗan takarar APC na mazabar Makera bayan an gudanar da zaɓen sulhu da ya samu halartar shugabannin jam’iyya, jami’an zaɓe da magoya baya.

Da yake bayyana sakamakon, jami’in tattara sakamakon zaɓen, Injiniya Ezekiel Samuel Gode, ya ce Liman ya zama ɗan takara ba tare da hamayya ba bayan amincewa da shi a matsayin ɗan takarar sulhu guda ɗaya na mazabar.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Bayan karɓar sakamakon tabbatarwa daga rumfunan zaɓe guda biyar, kuma babu wani ɗan takara da ya tsaya takara tare da shi, ina ayyana Hon. Liman Tahiru a matsayin wanda aka tabbatar kuma aka dawo da shi a matsayin ɗan takarar APC na mazabar Makera.”

Haka zalika, Mataimakin Shugaban Majalisar, Hon. Barr. Magaji Henry Danjuma, ya samu tikitin APC na mazabar Kagarko bayan mambobin jam’iyyar daga gundumomi daban-daban sun tabbatar da takararsa ba tare da hamayya ba.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.

Jami’in zaɓen APC, Abdulrahman Ibrahim Apo Jere, ne ya sanar da nasarar Danjuma a cibiyar tattara sakamakon ƙaramar hukumar bayan kammala tsarin tabbatarwar.

Ita ma Shugabar Masu Rinjaye ta Majalisar, Hon. Munira Suleiman Tanimu, ta samu tikitin APC na mazabar Lere ta Gabas bayan an gudanar da zaɓen sulhu cikin lumana a gundumomi shida na mazabarta.

Jami’in zaɓen mazabar Lere ta Gabas, Hon. Aminu Yaro, ya sanar da ita a matsayin ‘yar takarar jam’iyyar bayan kammala zaɓen da aka gudanar a Saminaka.

A wani mataki da ake ganin na ƙarfafa haɗin kan jam’iyya gabanin zaɓen shekarar 2027, wasu masu neman takarar kujerun Majalisar Dokokin Jihar Kaduna a ƙarƙashin APC sun janye daga takara tare da bayyana goyon bayansu ga ‘yan takarar sulhu na jam’iyyar.

Da yake jawabi a madadin waɗanda suka janye a Kaduna, Dakta Abdulrazaq Shuibu Labbo, mai neman takarar mazabar Kaka/Gogi ta Birnin Gwari, ya ce sun ɗauki matakin ne bayan tattaunawa da shiga tsakani da Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya yi domin tabbatar da haɗin kai a cikin jam’iyyar.

APC
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ya Dace ‘Yan Arewa Su Ƙara Marawa Tinubu Baya Domin Kammala Wa’adi Na Biyu — Shehu Sani
APC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing
  • Sulaiman
    Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

MASU ALAKA

Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

June 11, 2026
Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.
Manyan Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.

June 11, 2026
Nijeriya da Habasha Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dawo Da Fursunonin Nijeriya Sama da 100
Labarai

Nijeriya da Habasha Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dawo Da Fursunonin Nijeriya Sama da 100

June 11, 2026
Next Post
Kawancen Sin Da Rasha Na Kara Tabbatar Da Amincincewa Da Junansu A Duniya

Kawancen Sin Da Rasha Na Kara Tabbatar Da Amincincewa Da Junansu A Duniya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

June 11, 2026
Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

June 11, 2026
An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

June 11, 2026
Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

June 11, 2026
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

June 11, 2026
Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.

Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.

June 11, 2026
Shugaban Sin Na Jagorantar Bunkasa Dangantakar Sin Da Koriya Ta Arewa A Sabon Zamani

Shugaban Sin Na Jagorantar Bunkasa Dangantakar Sin Da Koriya Ta Arewa A Sabon Zamani

June 11, 2026
Nijeriya da Habasha Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dawo Da Fursunonin Nijeriya Sama da 100

Nijeriya da Habasha Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dawo Da Fursunonin Nijeriya Sama da 100

June 11, 2026
Za A Kammala Aikin Bututun Iskar Gas Na AKK A Disambar 2024 – NNPC

Na Yi Matuƙar Mamakin Sammaci A Kaina – Mele Kyari

June 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.