Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Dahiru Liman; da Mataimakin Shugaban Majalisar, Magaji Henry Danjuma, tare da shugabar Masu Rinjaye ta Majalisar, Munira Suleiman Tanimu, sun zama ‘yan takarar Jamiyyar (APC) domin wakiltar mazabunsu bayan gudanar da tantancewar sulhu a sassa daban-daban na jihar.
An tabbatar da Hon. Dahiru Liman a matsayin ɗan takarar APC na mazabar Makera bayan an gudanar da zaɓen sulhu da ya samu halartar shugabannin jam’iyya, jami’an zaɓe da magoya baya.
Da yake bayyana sakamakon, jami’in tattara sakamakon zaɓen, Injiniya Ezekiel Samuel Gode, ya ce Liman ya zama ɗan takara ba tare da hamayya ba bayan amincewa da shi a matsayin ɗan takarar sulhu guda ɗaya na mazabar.
Ya ce, “Bayan karɓar sakamakon tabbatarwa daga rumfunan zaɓe guda biyar, kuma babu wani ɗan takara da ya tsaya takara tare da shi, ina ayyana Hon. Liman Tahiru a matsayin wanda aka tabbatar kuma aka dawo da shi a matsayin ɗan takarar APC na mazabar Makera.”
Haka zalika, Mataimakin Shugaban Majalisar, Hon. Barr. Magaji Henry Danjuma, ya samu tikitin APC na mazabar Kagarko bayan mambobin jam’iyyar daga gundumomi daban-daban sun tabbatar da takararsa ba tare da hamayya ba.
Jami’in zaɓen APC, Abdulrahman Ibrahim Apo Jere, ne ya sanar da nasarar Danjuma a cibiyar tattara sakamakon ƙaramar hukumar bayan kammala tsarin tabbatarwar.
Ita ma Shugabar Masu Rinjaye ta Majalisar, Hon. Munira Suleiman Tanimu, ta samu tikitin APC na mazabar Lere ta Gabas bayan an gudanar da zaɓen sulhu cikin lumana a gundumomi shida na mazabarta.
Jami’in zaɓen mazabar Lere ta Gabas, Hon. Aminu Yaro, ya sanar da ita a matsayin ‘yar takarar jam’iyyar bayan kammala zaɓen da aka gudanar a Saminaka.
A wani mataki da ake ganin na ƙarfafa haɗin kan jam’iyya gabanin zaɓen shekarar 2027, wasu masu neman takarar kujerun Majalisar Dokokin Jihar Kaduna a ƙarƙashin APC sun janye daga takara tare da bayyana goyon bayansu ga ‘yan takarar sulhu na jam’iyyar.
Da yake jawabi a madadin waɗanda suka janye a Kaduna, Dakta Abdulrazaq Shuibu Labbo, mai neman takarar mazabar Kaka/Gogi ta Birnin Gwari, ya ce sun ɗauki matakin ne bayan tattaunawa da shiga tsakani da Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya yi domin tabbatar da haɗin kai a cikin jam’iyyar.















Discussion about this post