ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Da Wasu Jiga-jigan APC Sun Samu Tikitin APC Ta Hanyar Sulhu

by Shehu Yahaya and Sulaiman
2 months ago
APC

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Dahiru Liman; da Mataimakin Shugaban Majalisar, Magaji Henry Danjuma, tare da shugabar Masu Rinjaye ta Majalisar, Munira Suleiman Tanimu, sun zama ‘yan takarar Jamiyyar (APC) domin wakiltar mazabunsu bayan gudanar da tantancewar sulhu a sassa daban-daban na jihar.

An tabbatar da Hon. Dahiru Liman a matsayin ɗan takarar APC na mazabar Makera bayan an gudanar da zaɓen sulhu da ya samu halartar shugabannin jam’iyya, jami’an zaɓe da magoya baya.

Da yake bayyana sakamakon, jami’in tattara sakamakon zaɓen, Injiniya Ezekiel Samuel Gode, ya ce Liman ya zama ɗan takara ba tare da hamayya ba bayan amincewa da shi a matsayin ɗan takarar sulhu guda ɗaya na mazabar.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Bayan karɓar sakamakon tabbatarwa daga rumfunan zaɓe guda biyar, kuma babu wani ɗan takara da ya tsaya takara tare da shi, ina ayyana Hon. Liman Tahiru a matsayin wanda aka tabbatar kuma aka dawo da shi a matsayin ɗan takarar APC na mazabar Makera.”

Haka zalika, Mataimakin Shugaban Majalisar, Hon. Barr. Magaji Henry Danjuma, ya samu tikitin APC na mazabar Kagarko bayan mambobin jam’iyyar daga gundumomi daban-daban sun tabbatar da takararsa ba tare da hamayya ba.

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Jami’in zaɓen APC, Abdulrahman Ibrahim Apo Jere, ne ya sanar da nasarar Danjuma a cibiyar tattara sakamakon ƙaramar hukumar bayan kammala tsarin tabbatarwar.

Ita ma Shugabar Masu Rinjaye ta Majalisar, Hon. Munira Suleiman Tanimu, ta samu tikitin APC na mazabar Lere ta Gabas bayan an gudanar da zaɓen sulhu cikin lumana a gundumomi shida na mazabarta.

Jami’in zaɓen mazabar Lere ta Gabas, Hon. Aminu Yaro, ya sanar da ita a matsayin ‘yar takarar jam’iyyar bayan kammala zaɓen da aka gudanar a Saminaka.

A wani mataki da ake ganin na ƙarfafa haɗin kan jam’iyya gabanin zaɓen shekarar 2027, wasu masu neman takarar kujerun Majalisar Dokokin Jihar Kaduna a ƙarƙashin APC sun janye daga takara tare da bayyana goyon bayansu ga ‘yan takarar sulhu na jam’iyyar.

Da yake jawabi a madadin waɗanda suka janye a Kaduna, Dakta Abdulrazaq Shuibu Labbo, mai neman takarar mazabar Kaka/Gogi ta Birnin Gwari, ya ce sun ɗauki matakin ne bayan tattaunawa da shiga tsakani da Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya yi domin tabbatar da haɗin kai a cikin jam’iyyar.

APC
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass
APC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Sulaiman
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

MASU ALAKA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi
Labarai

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Next Post
Kawancen Sin Da Rasha Na Kara Tabbatar Da Amincincewa Da Junansu A Duniya

Kawancen Sin Da Rasha Na Kara Tabbatar Da Amincincewa Da Junansu A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.