Kamfanonin kasar Sin dake aikin hakar ma’adanai a kasar Zambia, sun jinjinawa sabuwar manufar gwamnatin kasar, wadda ta ba su damar biyan harajin hakar ma’adanai da kudin kasar Sin RMB.
Da yake bayyana gamsuwa da wannan manufa a jiya Laraba, yayin wani taron tattaunawa da ma’aikatar kudi da tsare-tsare ta Zambia ta shirya a birnin Lusaka, shugaban kungiyar kamfanonin Sin dake Zambia Wang Jingjun, ya ce kungiyarsu za ta yi cikakkiyar biyayya ga manufar gwamnatin, tare da tabbatar da biyan dukkanin harajin daidai kuma a kan lokaci.
Wang ya kara da cewa, wannan managarcin mataki ya samar da wata dama ta wanzar da daidaito a tsarin gudanar da hada-hadar kudade, zai kuma taimaka wajen dakile kalubalen sauyin darajar musayar kudade da a kan samu. Kazalika, manufar ta dace da burin gwamnatin kasar na nuna goyon baya ga kamfanonin, da aiwatar da mataki mai ma’ana na kara samar da daidaito, da kyakkyawan yanayi ga zuba jari na tsaron lokaci a kasar bisa hangen nesa.
A nasa tsokaci kuwa, ministan kudi da tsare-tsare na kasar ta Zambia Situmbeko Musokotwane, cewa ya yi gwamnatin kasar za ta ci gaba da samar da managarcin yanayi, a bude, kuma wanda za a iya hasashen makomarsa, don bunkasa moriyar sassa masu zaman kansu. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post