Li Shulei, babban jami’i a jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin (JKS) ya bayyana cewa, yin nazari sosai a game da mahangar Xi Jinping kan tsarin gurguzu mai salon kasar Sin a sabon zamani, shi ne mabudin fahimtar kasar Sin ta zamani.
Li, shugaban sashen wayar da kan jama’a na kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ya yi wannan tsokaci ne a lokacin da yake ganawa da wakilan kasashen waje da ke halartar wani taron kara wa juna sani na kasa da kasa game da mahangar Xi Jinping kan tsarin gurguzu mai salon kasar Sin a sabon zamani, a birnin Beijing.
Li ya ce, tun bayan babban taron jam’iyyar JKS karo na 18 a shekarar 2012, kwamitin tsakiya na jam’iyyar bisa jagorancin Kwamared Xi Jinping, ya shugabanci kasar Sin zuwa cimma nasarori da suka kafa tarihi, yana mai cewa, jam’iyyar JKS tana da muradin inganta musayar ra’ayi da koyo daga juna a tsakaninta da jam’iyyun siyasa na duk fadin duniya kan harkokin shugabancin kasa.
Mahalarta taron na kasashen waje sun bayyana cewa, wannan ziyara ta ba su damar shaida ci gaban da kasar Sin ta samu a fannoni da dama, tare da bayyana aniyarsu ta kara fahimtar mahanga, da daukar darasi daga hikima da karfin gudanarwa domin bunkasa ci gaban kasa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














