ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

by Yusuf Shuaibu
12 seconds ago
El-Rufai

Wani sautin murya da ake zargin na ɗan takarar gwamnan Jihar Kaduna ƙarƙashin jam’iyyar ADC, Alhaji Isa Ashiru, ya jawo cece-kuce tare da haifar da zazzafar muhawara a cikin jam’iyyar, inda masu goyon bayansa ke musunta cewa an ƙirƙiri sautin muryar ne kawai don a ɓata masa siyasa, yayin da magoya bayan tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ke tabbatar da biyayya gareshi.

An ruwaito cewa duk da cece-kucen da ake yi, matar El-Rufai, Aisha El-Rufai ta bayyana goyon bayanta ga ɗan takarar jam’iyyar ADC.

A cikin wani rubutu a shafin Facebook ɗinta da aka tabbatar, ta ce “Babu gudu ba ja da baya, babu miƙa wuya. Yin faɗa da gwagwarmaya ba ya hana mutuwa.

ADVERTISEMENT

“Sautin murya, wasiƙu, bidiyoyi duk abin da suke nunawa ko da Isa Ashiru zai yi mu’amala ba tare da Malam El-Rufai da iyalinsa. Na ce wa’adi ɗaya ne kawai, ba za a juyar ba, in Allah ya yarda,” ta rubuta.

An ce sautin muryar wadda aka yaɗa a kafafen sada zumunta, tana ɗauke da wani tattaunawar waya tsakanin Ashiru da wani dattijo daga kudancin Kaduna. A cikin muryar, ana zargin mai magana da ya yi watsi da El-Rufai, da ya kasance wani jigo a cikin jam’iyyar ADC.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

Duk da haka, ba a tabbatar da sahihancin sautin muryar ba, kuma har yanzu ba a tabbatar ba ko muryar Ashiru ce ko kuma shi ne ya yi maganganun da aka danganta masa.

A cikin sautin muryar, an ce mai magana ya bayyana cewa ya shiga ADC ne domin wata dabara ta siyasa wadda ke nufin samun tikitin takarar gwamna a jam’iyyar.

“Mun je ADC ne kawai don samun tikitin takarar gwamna a cikin jam’iyya domin mu samu nasara a zaɓe. Saboda jam’iyyar PDP ta rabu zuwa gida biyu. Wike yana jagorantar wani ɓangare, yayin da Tanimu Turaki ke jagorantar ɗaya ɓangaren, kuma duka ɓangarorin suna kotu,” a cikin sautin muryar.

Mai magana ya ƙara da cewa haɗuwarsa da El-Rufai ta samo asali ne daga buƙatar siyasa ba daga ra’ayin kansa ba.

Mai magana ya kuma zargi cewa an jingine El-Rufai a siyasa a cikin jam’iyya, yana kwatanta halin da yake ciki a yanzu a matsayin sakamakon abubuwan da ya aikata a baya.

Yayin da ake martani a cikin sautin muryar, wani shahararren ɗan ADC a Kaduna ta arewa kuma abokin Ashiru, wanda ya nemi a sakaya sunansa saboda bai samu izinin yin magana kan batun ba, ya yi watsi da sautin muryar tare da bayyana cewa na bogi ne.

“Ba mu yarda cewa muryarsa ce ba. A wannan zamani na fasahar sadarwa komai zai yiwu. An yi haka ne kawai don yunƙurin ɓata sunan Ashiru a gaban jama’a,” in ji abokin Ashiru.

Majiyar ta zargi ƴan siyasa masu hamayya da shirya kamfen na sharri kan Ashiru a daidai lokacin da ake fafatawar siyasa don zaɓen 2027.

Wata majiya cewa fitowar sautin muryar abun mamaki ne, ta ƙara da cewa, masoya tsohon gwamna sun haɗu a ranar Lahadi don tattauna sakamakon sautin muryan da aka saki da kuma tabbatar wa ƴan jam’iyya da ci gaba da goyon bayansu ga El-Rufai.

“A matsayinmu na masu biyayya ga El-Rufai a cikin jam’iyyar ADC, mun haɗu a yau don tattauna batun da kuma bayyana biyayyarmu ga El-Rufai. Za mu yi duk mai yuwuwa don kare martabarsa a Jihar Kaduna,” in ji majiyar.

Kazalika, jigon jam’iyyar ya ƙi yin ƙarin bayani, yana mai cewa za a gudanar da wani taro nan ba da jimawa ba don tantance matsayin masu biyayya ga El-Rufai a cikin jam’iyyar ADC.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton, Ashiru bai fitar da wata sanarwa a hukuma ba kan sautin muryar da aka yaɗa a kafafen sada zumunta.

An yi ƙoƙarin jin ta bakin Ashiru ta wayar salula amma abun ya ci tura, haka kuma bai amsa saƙonnin da aka tura masa ta WhatsApp ba.

A shekara ta 2015, Isa Ashiru ya ƙalubalanci El-Rufai a zaɓen fid da gwani na gwamnan jam’iyyar APC, amma ya sha kashi a hannun El-Rufai.

Bayan haka, ya koma jam’iyyar PDP, ya shiga zaɓen fid da gwani na jam’iyyar, ya kuma samu tikitin takarar gwamna a jam’iyyar. Ya kuma shan kashi a hannun El-Rufai.

A shekarar 2019, Ashiru ya samu tikitin takara a cikin jam’iyyar PDP kuma ya fafata da El-Rufai amma ya sha kaye a zaɓen. A shekarar 2023, ya sake fafatawa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP da Sanata Uba Sani a wani zaɓe mai tsauri, wanda shi ma ya sha kaye.

Yanzu ya koma jam’iyyar ADC kuma ya samu tikitin takarar gwamnan Jihar Kaduna na jam’iyyar karo na huɗu.

El-Rufai
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026

LABARAI MASU NASABA

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
Gwamna Dauda Ya Raba Buhunan Taki 72,000 Da Kayan Noma Kyauta Ga Manoman Zamfara

Gwamna Dauda Ya Raba Buhunan Taki 72,000 Da Kayan Noma Kyauta Ga Manoman Zamfara

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

July 11, 2026
Gwamnati Ta Shirya Gina Gidaje 20,000 Duk Shekara Haɗin Gwuiwar  Jamus

Gwamnati Ta Shirya Gina Gidaje 20,000 Duk Shekara Haɗin Gwuiwar Jamus

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.