Ɗan majalisar dokokin Amurka, Riley Moore, ya ce gwamnatin Amurka ƙarƙashin Shugaba Donald Trump za ta sa ido sosai kan zabɓen Nijeriya da za a yi a 2027.
Moore, wanda ya kasance ɗan jam’iyyar Republican da ke wakiltar West Ɓirginia, a yayin da yake amsa tambayoyi game da zaɓen Nijeriya, ya bayyana yadda za a gudanar da zaɓen a matsayin batun da Washington za ta sa ido sosai a kai.
Ya yi waɗannan maganganun a cikin wata hira da gidan talabijin na Noire TƁ, wanda aka ɗora a shafukan sada zumunta a ranar Lahadin da ta gabata.
Lokacin da aka tambaye shi ko Amurka za ta iya yin ƙarin abubuwa don tallafawa a samu sahihan zaɓe a Nijeriya, Moore ya ce, “Abin da zan ce shi ne, ina mai tabbas muku da cewa za mu saka ido wajen ganini sakamakon zaɓen da yadda zaɓe ke gudana da kuma yadda ake aiwatar da shi. Kuma wannan abu ne ni da gwamnati za mu mai da hankali sosai a kai.”
Ɗan majalisar dokokin Amurkan ya kuma bayyana cewa Majalisar Wakilan Amurka na duba wani ƙudirin kasafin kuɗi da ke ɗauke da wasu abubuwa dangane da Nijeriya, musamman kan ƴancin addini da taimakon tsaro na Amurka.
“Muna aiki kan ƙudirin Chris (Smith), wanda a fili ina ɗaya daga cikin masu goyon bayan ƙudirin. Amma zan ce, mafi muhimmanci, abin da mutane suke buƙatar su kula da shi shi ne, ƙudirin kasafin kuɗi da za mu gabatar a majalisa a yau,” in ji Moore.
A cewarsa, ƙudirin dokar da aka bayar yana ɗauke da wasu batutuwa masu ƙarfi da tsanani game da dangantakar Nijeriya da Amurka.
“Akwai yawan maganganun da na saka a wannan ƙudirin da suka shafi Nijeriya kan tsangwama ga Kiristoci da kuma taimakon tsaro ga gwamnatin Nijeriya, da matakan da dole za su ɗauka.
“Wannan ƙudirin dokar na iya zama doka. Mun shiriya tare da fatan amince da shi a yau. Kuma haka nan akwai wasu kalmomi masu ƙarfi da tsauri a cikin wannan ƙudirin da za su zama wajibi dangane da dangantakarmu da Nijeriya a gaba,” ya ƙara da cewa.
Moore ya ce zai ci gaba da tattaunawa da gwamnatin Trump kan batutuwan da suka shafi Nijeriya kuma ya bayyana cewa an tsara zai gana da shugaban ƙasar Amurka.
“Ina ci gaba da aiki tare da gwamnati kan matakan da za mu ɗauka na gaba. Gaskiya zan gana da Shugaba Trump a daren yau. Za mu ci abincin dare tare da shi da wasu ƴan majalisa, don haka, za mu ci gaba da tattaunawa da shi game da waɗannan batutuwa, kuma yana da matukar muhimmanci a gare shi,” in ji shi.
Moore shi ne ya fara gabatar da ƙudirin dokar ƴancin addini a Nijeriya ta 2026, wacce ya gabatar tare da ɗan majalisar dokokin Amurka, Chris Smith a watan Fabrairu.
Sabon ƙudirin dokar da ake shirin gabatarwa na nufin tilasta wa ministan harkokin wajen Amurka ya miƙa rahotanni lokaci-lokaci ga majalisar dokoki kan ƙoƙarin da ake yi don magance tsangwama ta addini da manyan ta’addanci a Nijeriya.
Ƙudirin dokar Smith da Moore na ba da shawarar a tantance yadda Nijeriya ke cika wajibai na ƴancin addini na duniya, taimakon tsaro na Amurka, takunkumi, tallafin jin kai, da matakan da gwamnatin Nijeriya ta ɗauka don kare al’ummomin da ke cikin haɗari da kuma gurfanar da masu kai hari.
Rahotanni sun bayyana cewa kwamitin majalisar Amurka a watan Afrilu 2026 ya amince da tanade-tanade da ke cikin ƙudin ƙarƙashin ma’aikatar harkokin waje da ke sanya ƙa’idoji masu tsauri da sharuɗɗa kan taimakon kuɗi ga Nijeriya.
Ƙudirin dokar, wadda aka tura wa majalisar dokokin Amurka don yin nazari, ta tanadin cewa kaso 50 cikin ɗari na kuɗaɗen da aka ware wa Nijeriya a ƙarƙashin sharuɗɗan taimakon ƙasashen waje za a dakatar da su har sai an tabbatar cewa gwamnati na ɗaukar matakai masu tasiri don rage tashin hankali na addini.
Haka nan kuma ƙudirin ya buƙaci kuɗaɗe da zai taimaka wa binciken da shari’ar tashin hankali da ƙungiyoyin Fulani suka aikata.
Ya ce dole ne gwamnati ta taimaka wajen dawo da mutanen da aka tilasta musu barin gidajensu cikin aminci.













