Mataimakin zaunannen wakilin Sin dake MDD Sun Lei ya yi jawabi a gun taron kwamitin sulhun MDD kan batun nukiliya na kasar Iran da aka gudanar a jiya 10 ga wannan wata, inda ya nemi a tabbatar da tsagaita bude wuta a yankin Gabas ta Tsakiya.
Sun Lei ya bayyana cewa, Amurka da Iran sun sanya hannu kan takardar fahimtar juna, don haka, an samu sassaucin yanayin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya, duk da a yanzu dai an dakatar da tsagaita bude wuta, inda hakan ya kawo cikas ga yin shawarwari a tsakaninsu. Kasar Sin ta kalubalanci bangarorin da abin ya shafa da su kawar da abin da ke kawo cikas, da watsi da amfani da karfin soja, da tabbatar da aiki da takardar fahimtar juna, da cimma daidaito kan warware batun bisa bukatunsu, da soke takunkumin da aka saka wa kasar Iran cikin hanzari, da kuma sa-kaimi ga warware batun ta hanyar siyasa.
Hakazalika, Sun Lei ya yi jawabi a gun babban taron MDD kan binciken batun shimfida zaman lafiya mai dorewa a jiya 10 ga wannan wata, inda ya jaddada cewa, ya kamata MDD ta maida aikin samun bunkasa a gaban komai yayin da ake gudanar da aikin shimfida zaman lafiya, da maida hankali ga fannonin zaman rayuwar jama’a ciki har da yaki da talauci, da ba da ilmi, da samar da aikin yi, da kiwon lafiya, da samar da hidimomin yau da kullum da sauransu, inda ta hakan jama’a za su nuna kyakkyawan fata ga yanayin zaman lafiya da jin dadin rayuwarsu baki daya, kana za a taimaka wa kasashensu wajen aza tubalin tattalin arziki da zamantakewar al’umma don shimfida zaman lafiya mai dorewa. (Zainab Zhang)













