Kasar Sin ta ce ba ta amince kasashen dake da huldar diplomasiyya da ita su cimma yarjejeniya a hukumance ko wadda za ta shafi cikakken ‘yancinta da yankin Taiwan ba.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jiakun ne ya bayyana hakan lokacin da yake mayar da martani game da yarjejeniyar cinikayya da aka cimma a baya-bayan nan tsakanin Amurka da yankin Taiwan na Sin, yana cewa ya kamata Amurka ta kiyaye ka’idar kasar Sin daya tak da sanarwoyin hadin gwiwa 3 dake tsakaninta da kasar Sin.
Har ila yau, kakakin ya ce kasar Sin ta yi imanin cewa bai kamata a yi hadin gwiwa tsakanin kasashe don musgunawa ko illata muradun wata kasa ba, haka kuma bai kamata irin wannan hadin gwiwa ya zama mai barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankalin wani yanki ba.
Guo Jiakun ya bayyana haka ne yayin taron manema labarai na yau Juma’a, lokacin da aka nemi ya yi tsokaci kan yarjejeniyar tsaro da aka cimma tsakanin Japan da Philippines dake da nufin bunkasa taimakekeniyar kayayyakin soji a tsakaninsu. (FMM)














Discussion about this post