Da tsakar dare, tan 24 na Tuffa (apples) daga kasar Afirka ta Kudu ya zama rukuni na farko na kayan da aka shigo da su kasar Sin a karkashin muhimmiyar manufar da aka bullo da ita, yayin da kasar Sin ta fadada shirin soke harajin kwastam ga dukkan kasashen Afirka 53 da ke da huldar diflomasiyya da ita.
Wannan manufar, ta fara aiki ne daga yau 1 ga watan Mayu.Kayan, wadda jami’an kwastam na Shenzhen suka tantance tare da amincewa da su cikin hanzari da safiyar yau Jumma’a, za a shigar da su ne manyan kantuna da kasuwannin sayar da kayayyaki a fadin kasar Sin.
Wadannan Tuffa na Afirka ta Kudu, an soke musu biyan kudin haraji daga kashi 10 cikin 100 zuwa sifili, wanda hakan ya karfafa gasa ta fuskar farashinsu a kasuwar kasar Sin.
Tun daga ranar 1 ga watan Disambar 2024 dai, kasar Sin ta fara aiwatar da manufar soke harajin kwastam ga kasashe masu karancin ci gaba da ke da alakar diflomasiyya da ita, ciki har da kasashen Afirka 33 masu karancin ci gaba.
Sabuwar manufar soke harajin kwastam, wani babban mataki ne da zai kara kuzari ga hadin gwiwar ciniki da saka hannun jari tsakanin Sin da Afirka da kuma ci gaban Afirka. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post