Jirgin farko na aikin jajji na 2026 daga Nijeriya zai tashi daga filin jirgin saman Gateway na Abeokuta, Babban Birnin Jihar Ogun, a ranar 3 ga Mayu, 2026, a jirgin FlyNas
An dai bayyana hakan a cikin wata sanarwa da mataimakiyar daraktan yada labarai ta hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya (NAHCON), Fatima Sanda Usara, ta fitar a jiya.
Wannan yana nuni da cewa a karon farko alhazan Jihar Ogun za su tashi daga babban birnin jihar bayan gyara filin jirgin sama.
Sauran jiragen sama da za su tashi a ranar guda su ne Umza da Mad Air daga Abuja, tare da fasinjojin Jihar Kogi da Nasarawa, bi da bi, Air Peace daga Legas tare da fasinjojin Jihar Oyo, da wani jirgin FlyNas daga Birnin Kebbi.
Saboda haka, hukumar NAHCON, ciki har da mambobin wucin gadi na tawagar likitoci ta kasa, sun tashi jiya don shirya tarbar alhazan Nijeriya.
NAHCON ta shawarci jirgin sama da za su yi jigilar alhazan cewa kowanne jigila zai gudana ne sau daya a yankin daya a lokaci daya. Da zarar an kammala jigilar jirgin daga yanki daya kuma za a koma na gaba, ba zai koma wannan yanki ba. Duk maniyyacin ya rasa jirgin da aka tsara a wannan yanki dole ya dauki sakamakon matsawa zuwa na gaba da ake da shi. Sauran matsaloli sun hada da jira har sai an sake hada su don tafiya.
“Na biyu, ku sani cewa alhazai dole ne su yi tafiya cikin kungiyarsu ta mutum 45, wadanda an riga an shirya katunan Nusuk dinsu lokacin da suka isa Saudiyya. Saboda haka, ana ba kowane mai yin aikin hajji shawarar ya tabbatar da sanin mambobin kungiyarsu kafin tafiyar.
“Haka kuma, ana shawartar masu aikin hajji su samo bayanan tuntubar shugabannin kungiyoyinsu da jami’in jiha ko jami’an jiha da za su raka taimaka musu wajen tafiya.”
Shugaban NAHCON, Ambasada Isma’il Abba Yusuf, ya tabbatar wa alhazan ‘yan Nijeriya cewa hukumar ta gudanar da dukkan shirye-shirye da suka dace don tabbatar da aikin hajji na 2026 ya gudana cikin sauki kuma cikin nasara.















Discussion about this post