Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta ce tsawaita da ta’azzarar rikici bai dace da muradun kowa ba, tana mai kira ga dukkan bangarori su taka muhimmiyar rawa wajen sassauta yanayin da ake ciki da ingiza hawa teburin sulhu.
Kakakin ma’aikatar Mao Ning ce ta bayyana haka a yau Talata, yayin taron manema labarai na yau da kullum, lokacin da take amsa tambaya game da kalaman shugaba Trump na jiya cewa, za a iya gamawa da Iran a dare daya, kuma daren ka iya zama yammacin ranar Talata, watau lokacin cikar wa’adin da ya dibar wa Iran na cimma yarjejeniya da bude Mashigin Hormuz.
Har ila yau, Mao Ning ta musanta kalaman tsohon jakadan Amurka a Sin Nicholas Burns, game da matsayar Sin kan Iran da Venezuela. Ta ce komai a bayyane yake game da batutuwan da suka shafi Iran da Venezuela, haka zalika matsayar kasar Sin.
Ta kara da cewa, bisa ra’ayin babakere na Amurka, Nicholas Burns ya yi fatali da ainihin musabbabin batutuwan, ya zabi nuna wa Sin yatsa, tare da jirkitawa da bata matsaya mai ma’ana da adalci ta zaman lafiya ta Sin, inda yake neman haddasa fitina tsakanin Sin da kasashen da batun ya shafa. (Fa’iza Mustapha)














Discussion about this post