ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ADC Reshen Kaduna Ta Buƙaci Gwamnati Ta Daina Tsangwamar El-Rufai

by Muhammad
2 months ago
ADC

Jam’iyyar ADC reshen Jihar Kaduna ta buƙaci gwamnati da ta dakatar da abin da ta kira ci gaba da tsanantawa da muzgunawa da daukar matakan siyasa da ake ɗauka kan tsohon gwamnan jihar, Nasir Ahmed El-Rufai, da sauran shugabannin adawa a jihar da ma ƙasa baki ɗaya.

Da yake magana a wani taron manema labarai da aka gudanar a Kaduna ranar Talata, tsohon kwamishinan ilimi na jihar, Sani Bello, wanda ya yi magana a madadin shugabannin ADC na jihar, ya yi kira da a mutunta doka ba tare da gundaya wani sharaɗi ba, ciki har da bin ƙa’idojin shari’a da kuma kare martabar kotuna.

  • El-Rufai Ya Ƙaryata Rahoton Goyon Bayan Yanki Ko Wani Mutum A Zaɓen 2027
  • Kwamitin Zartarwa Na ADC Na Ƙasa Ya Yi Watsi Da Bangaran David Mark Da Bala Gombe, Ya Naɗa Shugabancin Riƙo

Bello ya buƙaci a kawo ƙarshen amfani da hukumomin tsaro da na yaƙi da cin hanci da rashawa wajen cimma muradun siyasa na ɓangarenci.

ADVERTISEMENT

A cewar shugabannin ADC, sun buƙaci a dawo da cikakken tsarin dimokuraɗiyya, ciki har da ‘yancin siyasa, ‘yancin jam’iyyu, da za su ci ‘yancin kansu.

Ya ce, “Wannan bayani ya biyo bayan nazari mai zurfi kan abubuwan da ke faruwa a baya-bayan nan, waɗanda ke nuna wani yanayi mai tayar da hankali na amfani da hukumomin gwamnati ba daidai ba da watsi da bin ƙa’idojin shari’a, da kuma raunana tsarin dimokuraɗiyya.”

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

Ya ƙara da cewa, “Dangane da haka, shugabancin ADC na Jihar Kaduna na buƙatar a gaggauta dakatar da duk wata tsangwama da barazana da gurfanar da Mallam Nasir Ahmed El-Rufai da sauran ‘yan adawa a gaban kotu bisa dalilan siyasa. Haka kuma, a saki duk wanda aka tsare ba bisa ka’ida ba, ko kuma a gudanar da shari’a cikin gaskiya da adalci.”

Bello ya jaddada cewa dimokuraɗiyya tana bunƙasa ne idan akwai adawa mai ƙarfi, mutunta haƙƙoƙin ɗan adam, da kuma aiwatar da adalci ba tare da son kai ba.

Ya ce halin da ake ciki a yanzu na barazana ga waɗannan muhimman ginshiƙai, tare da iya raunana amincewar jama’a ga gwamnati da cibiyoyin dimokuraɗiyya.

A ƙarshe, jam’iyyar ADC ta yi kira ga hukumomin da abin ya shafa, ƙungiyoyin fararen hula, da kuma ƙasashen duniya da su lura da halin da ake ciki tare da ɗaukar matakan da suka dace domin kare dimokuraɗiyya, adalci da bin doka a Jihar Kaduna da Nijeriya gaba ɗaya.

ADC
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
Amurka Da Iran Sun Amince Da Tsagaita Wuta Na Mako Biyu

Amurka Da Iran Sun Amince Da Tsagaita Wuta Na Mako Biyu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.