Jam’iyyar ADC reshen Jihar Kaduna ta buƙaci gwamnati da ta dakatar da abin da ta kira ci gaba da tsanantawa da muzgunawa da daukar matakan siyasa da ake ɗauka kan tsohon gwamnan jihar, Nasir Ahmed El-Rufai, da sauran shugabannin adawa a jihar da ma ƙasa baki ɗaya.
Da yake magana a wani taron manema labarai da aka gudanar a Kaduna ranar Talata, tsohon kwamishinan ilimi na jihar, Sani Bello, wanda ya yi magana a madadin shugabannin ADC na jihar, ya yi kira da a mutunta doka ba tare da gundaya wani sharaɗi ba, ciki har da bin ƙa’idojin shari’a da kuma kare martabar kotuna.
- El-Rufai Ya Ƙaryata Rahoton Goyon Bayan Yanki Ko Wani Mutum A Zaɓen 2027
- Kwamitin Zartarwa Na ADC Na Ƙasa Ya Yi Watsi Da Bangaran David Mark Da Bala Gombe, Ya Naɗa Shugabancin Riƙo
Bello ya buƙaci a kawo ƙarshen amfani da hukumomin tsaro da na yaƙi da cin hanci da rashawa wajen cimma muradun siyasa na ɓangarenci.
A cewar shugabannin ADC, sun buƙaci a dawo da cikakken tsarin dimokuraɗiyya, ciki har da ‘yancin siyasa, ‘yancin jam’iyyu, da za su ci ‘yancin kansu.
Ya ce, “Wannan bayani ya biyo bayan nazari mai zurfi kan abubuwan da ke faruwa a baya-bayan nan, waɗanda ke nuna wani yanayi mai tayar da hankali na amfani da hukumomin gwamnati ba daidai ba da watsi da bin ƙa’idojin shari’a, da kuma raunana tsarin dimokuraɗiyya.”
Ya ƙara da cewa, “Dangane da haka, shugabancin ADC na Jihar Kaduna na buƙatar a gaggauta dakatar da duk wata tsangwama da barazana da gurfanar da Mallam Nasir Ahmed El-Rufai da sauran ‘yan adawa a gaban kotu bisa dalilan siyasa. Haka kuma, a saki duk wanda aka tsare ba bisa ka’ida ba, ko kuma a gudanar da shari’a cikin gaskiya da adalci.”
Bello ya jaddada cewa dimokuraɗiyya tana bunƙasa ne idan akwai adawa mai ƙarfi, mutunta haƙƙoƙin ɗan adam, da kuma aiwatar da adalci ba tare da son kai ba.
Ya ce halin da ake ciki a yanzu na barazana ga waɗannan muhimman ginshiƙai, tare da iya raunana amincewar jama’a ga gwamnati da cibiyoyin dimokuraɗiyya.
A ƙarshe, jam’iyyar ADC ta yi kira ga hukumomin da abin ya shafa, ƙungiyoyin fararen hula, da kuma ƙasashen duniya da su lura da halin da ake ciki tare da ɗaukar matakan da suka dace domin kare dimokuraɗiyya, adalci da bin doka a Jihar Kaduna da Nijeriya gaba ɗaya.














Discussion about this post