ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ADC Reshen Kaduna Ta Buƙaci Gwamnati Ta Daina Tsangwamar El-Rufai

by Muhammad
4 months ago
ADC

Jam’iyyar ADC reshen Jihar Kaduna ta buƙaci gwamnati da ta dakatar da abin da ta kira ci gaba da tsanantawa da muzgunawa da daukar matakan siyasa da ake ɗauka kan tsohon gwamnan jihar, Nasir Ahmed El-Rufai, da sauran shugabannin adawa a jihar da ma ƙasa baki ɗaya.

Da yake magana a wani taron manema labarai da aka gudanar a Kaduna ranar Talata, tsohon kwamishinan ilimi na jihar, Sani Bello, wanda ya yi magana a madadin shugabannin ADC na jihar, ya yi kira da a mutunta doka ba tare da gundaya wani sharaɗi ba, ciki har da bin ƙa’idojin shari’a da kuma kare martabar kotuna.

  • El-Rufai Ya Ƙaryata Rahoton Goyon Bayan Yanki Ko Wani Mutum A Zaɓen 2027
  • Kwamitin Zartarwa Na ADC Na Ƙasa Ya Yi Watsi Da Bangaran David Mark Da Bala Gombe, Ya Naɗa Shugabancin Riƙo

Bello ya buƙaci a kawo ƙarshen amfani da hukumomin tsaro da na yaƙi da cin hanci da rashawa wajen cimma muradun siyasa na ɓangarenci.

ADVERTISEMENT

A cewar shugabannin ADC, sun buƙaci a dawo da cikakken tsarin dimokuraɗiyya, ciki har da ‘yancin siyasa, ‘yancin jam’iyyu, da za su ci ‘yancin kansu.

Ya ce, “Wannan bayani ya biyo bayan nazari mai zurfi kan abubuwan da ke faruwa a baya-bayan nan, waɗanda ke nuna wani yanayi mai tayar da hankali na amfani da hukumomin gwamnati ba daidai ba da watsi da bin ƙa’idojin shari’a, da kuma raunana tsarin dimokuraɗiyya.”

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Ya ƙara da cewa, “Dangane da haka, shugabancin ADC na Jihar Kaduna na buƙatar a gaggauta dakatar da duk wata tsangwama da barazana da gurfanar da Mallam Nasir Ahmed El-Rufai da sauran ‘yan adawa a gaban kotu bisa dalilan siyasa. Haka kuma, a saki duk wanda aka tsare ba bisa ka’ida ba, ko kuma a gudanar da shari’a cikin gaskiya da adalci.”

Bello ya jaddada cewa dimokuraɗiyya tana bunƙasa ne idan akwai adawa mai ƙarfi, mutunta haƙƙoƙin ɗan adam, da kuma aiwatar da adalci ba tare da son kai ba.

Ya ce halin da ake ciki a yanzu na barazana ga waɗannan muhimman ginshiƙai, tare da iya raunana amincewar jama’a ga gwamnati da cibiyoyin dimokuraɗiyya.

A ƙarshe, jam’iyyar ADC ta yi kira ga hukumomin da abin ya shafa, ƙungiyoyin fararen hula, da kuma ƙasashen duniya da su lura da halin da ake ciki tare da ɗaukar matakan da suka dace domin kare dimokuraɗiyya, adalci da bin doka a Jihar Kaduna da Nijeriya gaba ɗaya.

ADC
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Amurka Da Iran Sun Amince Da Tsagaita Wuta Na Mako Biyu

Amurka Da Iran Sun Amince Da Tsagaita Wuta Na Mako Biyu

LABARAI MASU NASABA

ADC

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
ADC

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
ADC

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.