Yayin taron majalisar kare hakkin dan Adam ta MDD da aka yi jiya Juma’a, wakilin kasar Sin ya yi Allah wadai da hare-haren da kasashen Amurka da Isra’ila suka kai kan wata makaranta a kasar Iran.
Bisa bukatar kasashen Iran da Sin da Cuba, taro na 61 na majalisar kare hakkin dan Adam ta MDD (UNHCR), ya gudanar da muhawara kan hare-haren da aka kai makarantar ‘yan mata ta Shajareh Tayyebeh dake Minab na Iran, inda Jia Guide, zaunannen wakili kuma jakadan Sin a ofishin MDD da ke Geneva da sauran hukumomin kasa da kasa da ke kasar Switzerland, ya halarci taron tare da bayyana matsayar kasarsa kan lamarin.
Jia Guide ya yi tir da hare-haren kan makarantar ta Minab, wadanda suka yi sanadiyyar rayukan ‘yan mata 168, a matsayin mummunan laifi da ya keta hakkokin dan Adam kuma raini karara ga dokokin jin kai na kasa da kasa.
Ya kara da cewa, Amurka da Isra’ila sun kaddamar da hari kan Iran ba tare da sahalewar Kwamitin Sulhu na MDD ba, wanda shi ne tushen wannan ibtila’i.
Ya ce ya zama wajibi a girmama cikakken ‘yanci da tsaro da yankunan dukkan kasashe, yana cewa, Sin na tir da kausasan kalamai da ayyukan da ke keta dokokin kasa da kasa da kai hari kan fararen hula da kayayyakin da ba na soji ba.
Har ila yau, ya ce ya kamata a warware dukkan matsaloli ta hanyar shawarwari da tattaunawa, amma ba ta amfani da karfi ba. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post