Mahukuntan kasar Sin sun sanar a yau Talata cewa, kasar za ta fadada soke harajin kwastam ga dukkan kasashen Afirka da ke da huldar diflomasiyya da ita, daga ranar 1 ga watan Mayun shekarar 2026.
A cewar sanarwar da hukumar kwastam ta majalisar gudanarwar kasar Sin ta fitar, daga ranar 1 ga watan Mayun shekarar 2026 zuwa ranar 30 ga watan Afrilun 2028, kasar Sin za ta soke biyan harajin kwastam a karkashin tsarin harajin da aka fifita, ga kasashen Afirka 20 da suka kulla huldar diflomasiyya da ita, wadanda kuma ba su cikin jerin kasashe masu karancin ci gaba ko miskinan kasashe.Ga kasashe 33 na Afirka masu karancin ci gaba da ke da huldar diflomasiyya da ita kuwa, kasar Sin ta riga ta soke karbar harajin kwastam daga gare su da kashi 100 bisa 100 tun daga ranar 1 ga Disambar 2024.
Kasancewar za a fara aiwatar da manufar ta soke haraji da aka fadada a ranar Jumma’a mai zuwa, kasar Sin za ta zama kasa ta farko mai karfin tattalin arziki da za ta samar da cikakken tsarin soke haraji na bai-daya ga dukkan kasashen Afirka da ke da huldar diflomasiyya da ita, da ma daukacin kasashe masu karancin ci gaba da suke da alakar diflomasiyya da ita. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post