Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa,NDLEA, da Hukumar Kwastam ta Nijeriya, sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta haɗin gwiwa domin inganta ayyukansu da ƙarfafa haɗin kai tsakanin su.
An cimma yarjejeniyar ne a wani taro na manyan jami’ai da aka gudanar a hedikwatar NDLEA da ke Abuja a ranar 27 ga Afrilu, 2026, inda shugaban NDLEA, Mohamed Buba Marwa, da shugaban Hukumar Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi, suka sanya hannu kan sanarwar yarjejeniyar.
Mai magana da yawun NDLEA, Femi Babafemi, ya ce hukumomin biyu sun amince cewa ƙalubalen da ke tattare da laifukan ƙasa da ƙasa, musamman fataucin miyagun ƙwayoyi, na buƙatar haɗin kai mai ƙarfi da tsari na zamani.
Sabuwar yarjejeniyar na da nufin kawar da maimaita aiki, rage rikice-rikice tsakanin hukumomi, da samar da sauƙin musayar bayanan sirri.
Shugabannin hukumomin sun jaddada aniyarsu na ƙarfafa mutunta juna da ƙwarewa yayin gudanar da ayyukansu na kare tsaron ƙasa da sauƙaƙe kasuwanci na halal.
Sanarwar ta ƙunshi muhimman matakan haɗin gwiwa da suka haɗa da:
- Samar da ingantaccen tsarin musayar bayanan sirri domin dakile laifuka tun kafin su faru
- Kafa rundunonin haɗin gwiwa a wurare masu muhimmanci tare da cikakkun ƙa’idojin aiki
- Mutunta hurumin kowace hukuma domin kauce wa katsalandan
- Kafa kwamitin dindindin na haɗin gwiwa domin warware sabani cikin gaggawa
- Ƙarfafa aiki tare a tashoshin jiragen ruwa, filayen jiragen sama da iyakokin ƙasa
Marwa da Adeniyi sun bayyana cewa wannan haɗin gwiwa na da matuƙar muhimmanci ga ƙasa, domin zai taimaka wajen ƙarfafa yaƙi da safarar miyagun ƙwayoyi tare da inganta tsaron hanyoyin shiga da fita na Nijeriya.















Discussion about this post