ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kwalliya Za Ta Biya Kuɗin Sabulu Kan Sauye-sauyen Tinubu Na Inganta Tsaro A Nijeriya?

by Sadiq
2 weeks ago
Tinubu

A wani mataki na kawo ƙarshen ƙaruwar rashin tsaro a Nijeriya, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi gagarumin sauyi a shugabancin tsaro, ta hanyar bayar da umarnin ɗaukar sabbin ‘yan sanda da sojoji aiki, sannan ya janye ‘yan sanda daga tsaron manyan mutane.

Wannan sauyin ya haɗa da naɗin Janar Christopher Musa a matsayin sabon Ministan Tsaro, wanda ya maye gurbin Mohammed Badaru Abubakar, wanda ya yi murabus daga muƙamin saboda dalilai na rashin lafiya.

  • Tinubu Ba Zai Tattauna Da ’Yan Ta’adda Ba — Bwala
  • Mutum 4 Sun Mutu Yayin Da ’Yan Bindiga Sake Kai Hari Kogi

Haka kuma, shugaban ƙasa ya sake naɗa sabbin shugabannin sojojin ƙasa, ruwa da sama.

ADVERTISEMENT

Masana tsaro na ganin cewa wannan canjin shugabanci zai inganta haɗin gwiwar sojoji, dawo da ƙwarin gwiwar dakarun, da kawo sabbin dabaru a yaƙi da ‘yan ta’adda, ‘yan fashi da garkuwa da mutane, da sauran matsaloli da ke barazana da tsaro.

A lokaci guda, Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro a faɗin ƙasar na , inda ya ba da umarnin ɗaukar sabbin ‘yan sanda da sojoji aiki. Shirin ɗaukar ma’aikata ya tanadi ɗaukar sabbin jami’an tsaro, waɗanda za su samu horo a wurare daban-daban ciki har da sansanin horar da masu yi wa ƙasa hidima.

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Manufar wannan mataki ita ce ƙara yawan jami’an tsaro domin kare yankunan da suka fi fuskantar barazana, musamman ƙauyuka da garuruwa da ke fama da hare-hare.

A wani mataki da ya jawo hankalin jama’a, shugaban ƙasa ya umarci janye ‘yan sanda daga aikin kare manyan mutane, inda za a mayar da su aikin kare al’umma.

A yanzu manyan mutane za su dogara ne wajen samun kariya daga hukumar civil defence da wasu hukumomi.

Wannan mataki na nufin dawo da dubban jami’an tsaro daga kare manyan mutane zuwa aikin da ya fi muhimmanci na kare rayuwar talakawa da al’umma gaba ɗaya.

Sauyin Zai Iya Kawo Tasiri – Bukarti

Masana tsaro kamar irin su Bulama Bukarti, sun bayyana cewa wannan sauyi zai iya kawo babban tasiri wajen rage rashin tsaro a faɗin Nijeriya, musamman a lokacin da barazanar garkuwa da mutane da ‘yan ta’adda ke ƙaruwa.

“Mun sha kiran Gwamnatin Tarayya ta naɗa jakadu, ta kuma yi sauyi a fannin tsaro. Irin abin da shugaban ƙasa ya yi shi ne abin da ake tsammani tuntuni,” in ji Bukart.

Gwamnatin ta kuma ɗauki mataki na ƙarfafa dangantakar diplomasiyyar Nijeriya, inda Shugaba Tinubu ya aike sunayen mutane da Majalisar Dattawa za ta tantance a matsayin waɗanda zai yi muƙamin jakadu.

Wannan mataki na da nufin dawo da Nijeriya cikin sahun ƙasashen da ke da ƙarfin dangantaka da ƙasashen waje, wajen samun bayanai kan tsaro, haɗin gwiwar yaƙi da ta’addanci, da samun tallafi na ƙasashen waje, wajen horarwa da kayan aiki.

Masanan sun ce ƙarfafa dangantaka da ƙasashen waje na iya taimakawa wajen daƙile ayyukan ‘yan ta’adda da garkuwa da mutane da kuma sauran laifuka.

Wannan Lokaci Ne Mai Matuƙar Muhimmanci – Masani

Sai dai, masana tsaro sun yi gargaɗin cewa nasarar wannan shiri za ta dogara ne a kan: horarwa mai inganci, samun kuɗaɗen masu ɗorewa, gaskiya, da kuma magance tushen rashin tsaro kamar talauci, rashin aikin yi, rashin ingantaccen shugabanci da kuma rashin haɗin kai a tsakanin hukumomi.

“Wannan lokaci ne mai matuƙar muhimmanci,” in ji Dr. Musa Abubakar, ƙwararre a fannin harkar tsaro a Abuja.

“Ƙalubale yanzu shi ne tabbatar da manufofi a aikace, ganin cewa ‘yan sanda da aka mayar bakin aiki, da kowane aiki na soja ya kawo bambanci ga rayuwar ‘yan Nijeriya.”

Hakazalika, matakin zai iya kawo sauki a wuraren da aka fi fama da hare-haren ‘yan bindiga da garkuwa da mutane, inda sabbin jami’an tsaro za su ƙara yawan tsaro a ƙauyuka da garuruwa, da kuma rage hargitsi a manyan tituna.

Matakin Na Iya Zama Juyin Juya Hali

Masu sharhi kan harkokin tsaro sun bayyana cewa, wannan mataki na Tinubu na iya zama juyin juya hali ga tsarin tsaro a Nijeriya, musamman idan aka aiwatar da shi yadda ya kamata.

Yayin da Najeriya ke kallon wannan mataki, matakan gwamnatin Tinubu na iya zama wani juyin juya hali a yaƙi da matsalar tsaro ko kuma su kasance wani babban sauyi mai ɗaukar hankali ba tare da tasiri mai ɗorewa ba.

Amma idan aka aiwatar da wannan shiri da gaskiya, horo mai inganci, da kyakkyawan tsarin aiki, akwai yiwuwar Nijeriya za ta ga ingantaccen tsaro a cikin watanni masu zuwa, wanda zai taimaka wajen rage hare-haren ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga a faɗin ƙasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace
Rahotonni

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025
Tinubu Ya Nuna Kwarewa Da Gogewa A Sha’anin Mulkin Nijeriya – Bishir Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Nuna Kwarewa Da Gogewa A Sha’anin Mulkin Nijeriya – Bishir Dauda

December 19, 2025
Next Post
Menene Dalilin Da Ya Sa CAF Ba Ta Ɗauki Alƙalan Nijeriya A Gasar AFCON Ta 2025 Ba?

Menene Dalilin Da Ya Sa CAF Ba Ta Ɗauki Alƙalan Nijeriya A Gasar AFCON Ta 2025 Ba?

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.