ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kwalliya Za Ta Biya Kuɗin Sabulu Kan Sauye-sauyen Tinubu Na Inganta Tsaro A Nijeriya?

by Sadiq
7 months ago
Tinubu

A wani mataki na kawo ƙarshen ƙaruwar rashin tsaro a Nijeriya, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi gagarumin sauyi a shugabancin tsaro, ta hanyar bayar da umarnin ɗaukar sabbin ‘yan sanda da sojoji aiki, sannan ya janye ‘yan sanda daga tsaron manyan mutane.

Wannan sauyin ya haɗa da naɗin Janar Christopher Musa a matsayin sabon Ministan Tsaro, wanda ya maye gurbin Mohammed Badaru Abubakar, wanda ya yi murabus daga muƙamin saboda dalilai na rashin lafiya.

  • Tinubu Ba Zai Tattauna Da ’Yan Ta’adda Ba — Bwala
  • Mutum 4 Sun Mutu Yayin Da ’Yan Bindiga Sake Kai Hari Kogi

Haka kuma, shugaban ƙasa ya sake naɗa sabbin shugabannin sojojin ƙasa, ruwa da sama.

ADVERTISEMENT

Masana tsaro na ganin cewa wannan canjin shugabanci zai inganta haɗin gwiwar sojoji, dawo da ƙwarin gwiwar dakarun, da kawo sabbin dabaru a yaƙi da ‘yan ta’adda, ‘yan fashi da garkuwa da mutane, da sauran matsaloli da ke barazana da tsaro.

A lokaci guda, Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro a faɗin ƙasar na , inda ya ba da umarnin ɗaukar sabbin ‘yan sanda da sojoji aiki. Shirin ɗaukar ma’aikata ya tanadi ɗaukar sabbin jami’an tsaro, waɗanda za su samu horo a wurare daban-daban ciki har da sansanin horar da masu yi wa ƙasa hidima.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Manufar wannan mataki ita ce ƙara yawan jami’an tsaro domin kare yankunan da suka fi fuskantar barazana, musamman ƙauyuka da garuruwa da ke fama da hare-hare.

A wani mataki da ya jawo hankalin jama’a, shugaban ƙasa ya umarci janye ‘yan sanda daga aikin kare manyan mutane, inda za a mayar da su aikin kare al’umma.

A yanzu manyan mutane za su dogara ne wajen samun kariya daga hukumar civil defence da wasu hukumomi.

Wannan mataki na nufin dawo da dubban jami’an tsaro daga kare manyan mutane zuwa aikin da ya fi muhimmanci na kare rayuwar talakawa da al’umma gaba ɗaya.

Sauyin Zai Iya Kawo Tasiri – Bukarti

Masana tsaro kamar irin su Bulama Bukarti, sun bayyana cewa wannan sauyi zai iya kawo babban tasiri wajen rage rashin tsaro a faɗin Nijeriya, musamman a lokacin da barazanar garkuwa da mutane da ‘yan ta’adda ke ƙaruwa.

“Mun sha kiran Gwamnatin Tarayya ta naɗa jakadu, ta kuma yi sauyi a fannin tsaro. Irin abin da shugaban ƙasa ya yi shi ne abin da ake tsammani tuntuni,” in ji Bukart.

Gwamnatin ta kuma ɗauki mataki na ƙarfafa dangantakar diplomasiyyar Nijeriya, inda Shugaba Tinubu ya aike sunayen mutane da Majalisar Dattawa za ta tantance a matsayin waɗanda zai yi muƙamin jakadu.

Wannan mataki na da nufin dawo da Nijeriya cikin sahun ƙasashen da ke da ƙarfin dangantaka da ƙasashen waje, wajen samun bayanai kan tsaro, haɗin gwiwar yaƙi da ta’addanci, da samun tallafi na ƙasashen waje, wajen horarwa da kayan aiki.

Masanan sun ce ƙarfafa dangantaka da ƙasashen waje na iya taimakawa wajen daƙile ayyukan ‘yan ta’adda da garkuwa da mutane da kuma sauran laifuka.

Wannan Lokaci Ne Mai Matuƙar Muhimmanci – Masani

Sai dai, masana tsaro sun yi gargaɗin cewa nasarar wannan shiri za ta dogara ne a kan: horarwa mai inganci, samun kuɗaɗen masu ɗorewa, gaskiya, da kuma magance tushen rashin tsaro kamar talauci, rashin aikin yi, rashin ingantaccen shugabanci da kuma rashin haɗin kai a tsakanin hukumomi.

“Wannan lokaci ne mai matuƙar muhimmanci,” in ji Dr. Musa Abubakar, ƙwararre a fannin harkar tsaro a Abuja.

“Ƙalubale yanzu shi ne tabbatar da manufofi a aikace, ganin cewa ‘yan sanda da aka mayar bakin aiki, da kowane aiki na soja ya kawo bambanci ga rayuwar ‘yan Nijeriya.”

Hakazalika, matakin zai iya kawo sauki a wuraren da aka fi fama da hare-haren ‘yan bindiga da garkuwa da mutane, inda sabbin jami’an tsaro za su ƙara yawan tsaro a ƙauyuka da garuruwa, da kuma rage hargitsi a manyan tituna.

Matakin Na Iya Zama Juyin Juya Hali

Masu sharhi kan harkokin tsaro sun bayyana cewa, wannan mataki na Tinubu na iya zama juyin juya hali ga tsarin tsaro a Nijeriya, musamman idan aka aiwatar da shi yadda ya kamata.

Yayin da Najeriya ke kallon wannan mataki, matakan gwamnatin Tinubu na iya zama wani juyin juya hali a yaƙi da matsalar tsaro ko kuma su kasance wani babban sauyi mai ɗaukar hankali ba tare da tasiri mai ɗorewa ba.

Amma idan aka aiwatar da wannan shiri da gaskiya, horo mai inganci, da kyakkyawan tsarin aiki, akwai yiwuwar Nijeriya za ta ga ingantaccen tsaro a cikin watanni masu zuwa, wanda zai taimaka wajen rage hare-haren ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga a faɗin ƙasar nan.

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Menene Dalilin Da Ya Sa CAF Ba Ta Ɗauki Alƙalan Nijeriya A Gasar AFCON Ta 2025 Ba?

Menene Dalilin Da Ya Sa CAF Ba Ta Ɗauki Alƙalan Nijeriya A Gasar AFCON Ta 2025 Ba?

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.