Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta hana Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) amincewa ko halartar duk wani taron jam’iyyar ADC da wasu wakilan shugabancin riƙon ƙwarya na ADC ya shirya.
A hukuncin da Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta yanke ranar Laraba, kotun ta kuma hana tsohon shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, da wasu jiga-jigan jam’iyyar tsoma baki cikin ayyukan shugabannin jihohi da aka zaɓa wanda wa’adinsu bai ƙare ba.
Hukuncin ya kawo wani sabon salo a rikicin shugabanci da ya daɗe yana addabar ADC, wanda zai iya yin tasiri kan ikon tafiyar da tsarin jam’iyyar kafin manyan harkokin siyasa masu zuwa.
Wasu mutane bakwai ƙarƙashin jagorancin Norman Obinna ne suka shigar da ƙarar a madadin shugabannin jihohi da kwamitocin gudanarwa na ADC a faɗin ƙasar.
Sun ƙalubalanci halaccin matakan da shugabancin riƙon ƙwarya na ƙasa ya ɗauka, musamman yunkurin shirya tarukan jihohi ta hannun wani kwamiti da aka naɗa.
Masu ƙarar sun kafa hujjar cewa shugabancin riƙon ƙwaryar ba shi da hurumin kundin tsarin mulkin jam’iyyar na shirya taruka ko kafa kwamitoci domin hakan, suna masu cewa hukumomin da aka zaɓa bisa tsarin jam’iyyar ne kawai ke da ikon gudanar da irin waɗannan ayyuka.
Sun roƙi kotun da ta tabbatar da wa’adin shugabannin jihohin da ke kan mulki tare da hana duk wani tsarin da zai iya raunana ikonsu.















Discussion about this post