An gudanar da bikin mika katafariyar helkwatar kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ko ECOWAS ga kungiyar, aikin da kasar Sin ta samar da tallafin kudaden gudanarwa.
An gudanar da bikin ne a jiya Talata a birnin Abuja, fadar mulkin Najeriya. Aikin ya shaida babban ci gaba a fannin dunkulewar shiyyar yammacin Afirka da ma ingancin dangantakar Sin da kasashen nahiyar.
Ginin helkwatar ta ECOWAS wanda aka yiwa lakabi da “Eye of West Africa,” zai samar da zarafi na dunkule daukacin ayyukan hukumar gudanarwar kungiyar a wuri guda, ya kuma kunshi zauren majalisar dokoki da kotun al’umma ta kungiyar, wadanda a baya suke da ofisoshi a wurare daban daban a cikin birnin Abuja.
Da yake jawabi yayin bikin mika ginin ga ECOWAS, jakadan Sin a Najeriya Yu Dunhai, ya bayyana shi a matsayin muhimmin aiki mai shaida kyakkyawar danganta dake akwai tsakanin Sin da kasashen Afirka.
A nasa tsokacin kuwa, shugaban hukumar zartarwar kungiyar ECOWAS Omar Touray, jinjinawa ingancin ginin da kamfanin Sin ya gudanar ya yi, yana mai yabawa kammalar aikin kan lokaci duk da sarkakiyarsa. (Mai Fassara: Saminu Alhassan)















Discussion about this post