ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Ku Cusa Ɗabi’u Nagari A Zukatan ‘Ya’yanku”, Kiran Ministan Yaɗa Labarai Ga Iyaye

by Sulaiman
2 years ago
Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga iyaye da masu kula da yara da su jajirce wajen ganin sun cusa halaye masu kyau a zukatan ‘ya’yan su.

 

A wata sanarwa da Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai na ministan, Malam Rabiu Ibrahim, ya fitar a ranar Lahadi, an bayyana cewa ministan ya yi wannan kiran ne a Kaduna ranar Asabar, a wajen taron laccar watan Ramadan da NTA, FRCN, VON da NBC suka shirya, mai taken “Sauye-sauyen Iyali: Haƙƙoki Da Wajibai a Mahangar Musulunci.”

ADVERTISEMENT
  • Ku Yi Amanna Da Tinubu, Matsalolin Zu Su Zo Karshe, inji Ministan Yaɗa Labarai
  • ‘Yansanda Sun Cafke Mutum 3 Da Ake Zargi Da Yunkurin Yin Garkuwa Da Mutane A Bauchi

A jawabin nasa, Idris ya ce iyali suna da wani aiki mai tsarki na sanya ƙa’idojin aminci, tausayawa, da gaskiya, tare da sauran ɗabi’u nagari a zukatan ‘ya’yan su domin su tsara halayen su da shiryar da ayyukan su a tsawon rayuwa.

Ya ce: “Dabi’un na ƙwarai su ne ke tafiyar da yaran mu ta cikin sarƙaƙiyar rayuwar duniya, suna taimaka musu su bambance abu mai kyau da mara kyau da kuma bibiyar matsalolin ɗabi’a cikin haske da imani.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

“Ta hanyar koyar da waɗannan dabi’u a gidajen mu, muna ba yaran mu abubuwan da suke buƙata don zama masu riƙon amana da sanin ya-kamata a cikin al’umma.”

Ministan ya ƙara da cewa iyali sun kasance ginshiƙin al’umma, wanda ke tattare da addini, ɗabi’u, da al’adu da kuma ginshikin al’umma, wanda ke raya zuri’a mai zuwa tare da inganta zumuncin da zai wuce lokaci da yanayi.

Ya ce ma’aikatar sa na gab da ƙaddamar da Kundin Tsarin Martabar Nijeriya, wanda ya ƙunshi yarjejeniyar zamantakewa tsakanin wannan ƙasar da ‘yan ƙasar, kuma za ta zama wani tsari da manufa ta tsarin ƙimar ƙasa.

Ya ce, “Sabon tsarin, wanda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai ƙaddamar a bana, ya ƙunshi Alƙawurran Nijeriya da kuma Ƙa’idojin ‘Yan Ƙasa, waɗanda ke da ginshiƙai bakwai kowanne.

“Gwamnati na da niyyar shigar da waɗannan ɗabi’u cikin tsare-tsare na hukuma, da wanda ba na hukuma ba, da kuma na koyar da sana’o’i don tabbatar da cewa an cusa su a zukatan ‘yan ƙasa.”

Idris ya ce gwamnatin Tinubu ta ba da fifiko wajen aiwatar da tsare-tsare da shirye-shirye masu tallafawa da ƙarfafa iyali da kuma tabbatar da cewa kowane mutum ya samu damar yin rayuwa mai daɗi da kwanciyar hankali, tare da isassun damarmaki don cimma buƙatun sa da burin sa.

“Saboda haka ne gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta himmatu wajen samar da yanayi mai kyau ga ɗaukacin ‘yan Nijeriya ta hanyar aiwatar da sauye-sauyen kasafin kuɗi da na kuɗi da nufin bunƙasa tattalin arzikin ƙasa, rage talauci, da samar da cigaba mai ɗorewa.

“Sauye-sauyen da Mai Girma Shugaban Ƙasa ke aiwatarwa, ba wai martanin da ba a shirya masa ba ne ga matsalolin tattalin arzikin mu; tsare-tsare ne da aka yi tunani a kan su sosai don gudanar da su tare da cikakken Shirin Shiga Tsakani na Jama’a don rage raɗaɗin sauye-sauyen,” inji shi.

Ministan ya ce tare da sake fasalin Shirin Zuba Jari na Ƙasa, an ɓullo da wasu ƙarin tsare-tsare don tabbatar da gaskiya da riƙon amana wajen raba kuɗaɗe ga talakawa da marasa galihu a cikin al’umma, yana mai jaddada cewa daga yanzu za a tantance waɗanda za su amfana da Lambar Shaidarsu ta ɗan Ƙasa (NIN) da BVN ko asusun waya da aka tantance.

Ya ƙara da cewa a halin yanzu ana gudanar da sauyin yanayi a fannin noma, inda ya ce tawagar sa ta yi mamakin irin nasarorin da ake samu a noman rani a lokacin da suka gudanar da rangadi a wasu al’ummomin manoma a jihohin Kano da Jigawa.

“A ranar Alhamis, na jagoranci Tawagar Sadarwa ta Ƙasa, wadda ta ƙunshi manyan mashawartan Shugaban Ƙasa kan harkokin yaɗa labarai da sadarwa, da kuma manyan daraktoci na Hukumar Wayar Da Kan Jama’a ta Ƙasa (NOA), NTA, VON, da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), a rangadin aiki a jihohin Kano da Jigawa domin ganin yadda sauyin yanayi a fannin noma ke faruwa a sannu-sannu.

“Ziyarar da tawagar mu ta kai wa Shirin Noman Rani na Haɗeja mai samun goyon bayan Gwamnatin Tarayya da Bankin Duniya ya nuna yadda ake gagarumin noman shinkafa, zoɓo, da alkama, da dai sauran amfanin gona da manoman Jihar Jigawa suke nomawa, waɗanda duk shekara suke noma a bakin tekun kogin Haɗeja da Jama’are. Don Allah, dukkan mu mu rungumi noma da kiwo da fa’idar da suke da ita,” inji shi.

Labarai
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba
  • Sulaiman
    Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

MASU ALAKA

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa
Manyan Labarai

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai
Rahotonni

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila
Manyan Labarai

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

June 26, 2026
Next Post
Peng

Peng Liyuan Ta Yi Rangadin Aikin Rigakafi Da Shawo Kan Cutar Tarin Fuka A Birnin Changsha Na Lardin Hunan

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

June 26, 2026
Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026
Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Noma

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.