Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su zaɓi ’yan takara bisa la’akari da ayyukansu, kwarewarsu da cancantarsu, maimakon addininsu a babban zaɓen 2027.
Daurawa ya yi wannan kiran ne yayin wata hira da DW Hausa.Malamin ya ce ya kamata masu kaɗa ƙuri’a su fi mayar da hankali kan yadda ’yan takarar za su iya samar da shugabanci nagari da kuma irin tarihin ayyukansu a hidimar jama’a.
Ya ce, “Bai kamata batun ya kasance kan addini ba, sai dai wanda zai yi aiki, abin da mutumin zai iya yi, da kuma abin da ya taɓa yi.”
Daurawa ya bayyana cewa tsarin dimokuraɗiyyar Nijeriya bai ginu a kan addini ba, yana mai cewa Kundin Tsarin Mulkin kasar bai amince da jam’iyyun siyasa a matsayin ƙungiyoyin Musulunci ko Kiristanci ba.
Har ya yi tambaya da cewa, “Shin akwai wata jam’iyya da INEC ta yi wa rajista a matsayin jam’iyyar Musulunci ko ta Kiristanci, ko kuma wacce take da kundin manufofin addini?”
Ya ce ya kamata ’yan Nijeriya su samu ’yancin zaɓar duk ɗan takarar da suke ganin ya cancanta, ba tare da la’akari da tsarin tikitin da yake kai ba, ko Muslim-Muslim, Kirista-Kirista, Musulmi-Kirista ko Kirista-Musulmi.














