Sojojin rundunar haɗin gwiwa ta Operation FANSAN YAMMA sun ceto mutane 10 a wasu hare-hare daban-daban da suka gudanar a jihohin Sakkwato, Kebbi da Zamfara.
Rundunar sojin ta ce an gudanar da ayyukan ne tsakanin ranar 18 zuwa 19 ga watan Agustan 2026.
A Jihar Sakkwato, sojoji sun fafata da ‘yan ta’adda da suka yi musu kwanton ɓauna a ƙaramar hukumar Isa.
An ceto mutane biyar tare da sada su da iyalansu.
Haka kuma, an ƙwato babura biyu da ‘yan ta’addan suka bari yayin da suke tserewa.
A Jihar Kebbi, sojoji sun ceto mutane uku da aka yi garkuwa da su a ƙaramar hukumar Danko Wasagu.
A Jihar Zamfara kuma, sojoji sun kai ɗauki bayan samun rahoton ayyukan ‘yan ta’adda a ƙaramar hukumar Tsafe.
Hakan ya tilasta wa ‘yan ta’addan tserewa tare da barin mutane biyu da suka sace.
Mutanen biyu sun samu raunukan harbin bindiga, inda aka garzaya da su asibiti domin samun kulawar gaggawa.
Rundunar sojin ta ce ana ci gaba da ƙoƙarin gano ‘yan ta’addan da suka tsere, tare da roƙon jama’a su riƙa bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai domin taimaka wa ayyukan tsaro.














