Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Rabiu Musa Kwankwaso, ya miƙa saƙon ta’aziyya ga tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Bauchi, Baba Tela, bisa rasuwar ’ya’yansa biyu, Mustapha Tela da Ummi Tela, waɗanda suka rasu sakamakon wani mummunan hatsarin mota.
Kwankwaso ya bayyana saƙon ta’aziyyarsa ne cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X da aka tabbatar a ranar Litinin.
Ya bayyana lamarin a matsayin wani babban abin baƙin ciki da ya girgiza ba iyalan mamatan kaɗai ba, har ma da masarautar Katagum da daukacin al’ummar Jihar Bauchi.
A cikin saƙonsa, ya ce, “Ina miƙa ta’aziyyata ta musamman ga tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Baba Tela, bisa wannan babban rashi na ’ya’yansa, Mustapha da Ummi, waɗanda suka rasu a wani mummunan hatsarin mota.”
Kwankwaso ya kuma yi addu’ar Allah Ya jikansu da rahama, Ya gafarta musu kura-kuransu, tare da bai wa iyalansu haƙurin jure wannan babban rashi.













