An kaddamar da atisayen hadin gwiwa mai taken “Hadin gwiwar ayyuka kan teku-2026” tsakanin Sin da Rasha a wata tashar jiragen ruwan soji dake birnin Qingdao na lardin Shandong yau Litinin.
Bayan bikin kaddamar da atisayen, sojojin ruwa na kasashen biyu sun gudanar da atisayen ba da umarni da hadin gwiwar dabarun yaki, kuma hedikwatar rundunar hadin gwiwa ta gudanar da tattaunawa mai zurfi kan muhimman batutuwan dake cikin atisayen na kan teku.
Abu na gaba shi ne, jiragen ruwan da suka shiga atisayen za su gudanar da atisayen leken asiri na hadin gwiwa, da atisayen kariya daga makamai masu linzami, da sauran batutuwa a cikin yankunan teku da sararin samaniya dake kusa da birnin Qingdao, sannan za su gudanar da horon amfani da makamai a zahiri. (Safiyah Ma)













