ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
Kisa

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

Shugaban Kwamitin Majalisar Wakilai kan Al’amuran Sojin Ruwa, Yusuf Adamu Gagdi, ya bayyana cewa duk wani ɗan bindiga ko ɗan ta’adda da aka kama da laifin kisan mutane ba shi da hurumin samun afuwa ko shirin gyaran hali (rehabilitation), face dai hukuncin kisa ta hanyar rataya.

Yusuf Gagdi, wanda ke wakiltar mazaɓar Pankshin/Kanke/Kanam daga Jihar Plateau a majalisar tarayya, ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi ga manema labarai kan yadda za a magance matsalar rashin tsaro da ke addabar shiyyar Arewa da sauran sassan ƙasar nan. Ɗan majalisar ya soki tsarin da gwamnati ke amfani da shi na sauya wa tubabbun ‘yan ta’adda halayya (irin su tsoffin mambobin Boko Haram ko ‘yan bindiga), inda ya bayyana cewa wannan tsari yana ƙara wa miyagu karfin gwiwar ci gaba da kisan jama’a ne ba tare da tsoron komai ba.

Gagdi ya jaddada cewa dokar ƙasa ta tanadi hukuncin kisa ga duk wanda aka samu da laifin kisan kai, saboda haka babu adalci a ce an kashe manoma ko ‘yan ƙasa maras laifi sannan a kama maharin a riƙa ciyar da shi da kuɗin haraji da sunan canza masa halayya. Ya yi kira da babbar murya ga Gwamnatin Tarayya da hukumomin shari’a da su gaggauta aiwatar da hukuncin kisa na gaggawa ga duk wani mai garkuwa da mutane ko ɗan bindiga da aka kama domin ya zama izina ga sauran masu shirin tafka irin wannan aika-aika.

ADVERTISEMENT

Wannan tsokaci na Yusuf Gagdi ya zo ne a daidai lokacin da al’ummomin Jihar Filato da sauran jihohin makwabta ke ci gaba da fuskantar hare-haren dare na ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane. Jam’ian majalisar da masana tsaro da dama sun daɗe suna muhawara kan dacewa ko rashin dacewar shirin afuwa ga ‘yan ta’adda, inda yawancin ‘yan ƙasa ke goyon bayan matakin Gagdi na cewa a hukunta kowa daidai da laifin da ya aikata domin dawo da amincin doka a ƙasar baki ɗaya.

Kisa
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano
  • Abubakar Sulaiman
    Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu
  • Abubakar Sulaiman
    ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa
  • Abubakar Sulaiman
    Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

MASU ALAKA

Kisa
Manyan Labarai

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Manyan Labarai

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Kisa
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Next Post
Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

LABARAI MASU NASABA

Kisa

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Kisa

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026
Kisa

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

July 27, 2026
Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

July 27, 2026
Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

July 27, 2026
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026
Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.