Babbar Kotun Tarayya da ke zama a birnin Abuja ta amince da ɗage ranar yanke hukunci na ƙarshe dangane da ƙarar da Hukumar Yaƙi da Yi wa Tattalin Arzikin Ƙasa Ta’annati (EFCC) ta shigar, tana neman a ba ta damar kwace wasu manyan kadarori guda hamsin da bakwai (57) na tsohon Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Ƙasa (AGF), Abubakar Malami (SAN).
Alƙalin kotun, Mai Shari’a Emeka Nwite, shi ne ya sanar da ɗage zaman bayan da lauyoyin ɓangaren Malami da na hukumar EFCC suka kammala gabatar da hujjojinsu na ƙarshe a gaban kotun. Hukumar EFCC tana neman babban hukunci na dindindin (final forfeiture) kan waɗannan kadarori, waɗanda suka haɗa da manyan gidajen alfarma, otal-otal, da filaye da ke birnin Abuja, Kano, da jihar Kebbi, bayan da ta zargi cewa tsohon ministan ya mallake su ne ta hanyar amfani da kuɗaɗen haram da kuma karkatar da dukiyar ƙasa a lokacin da yake kan mulki.
A nasa ɓangaren, Abubakar Malami ta hanyar babban lauyansa, Mista Wahab Shittu (SAN), ya musanta dukan waɗannan zargi na EFCC baki ɗaya. Lauyan ya gabatar da takaddun kariya inda ya bayyana cewa yawancin waɗannan kadarori an same su ne ta hanyar halal kafin da kuma lokacin da Malami yake riƙe da madafun iko, kuma matakin na EFCC ya saɓa wa ƙa’idojin shari’a.
Wannan shari’a tana ci gaba da ɗaukar hankalin al’ummar ƙasar nan duba da cewa Abubakar Malami ya kasance ɗaya daga cikin manyan jiga-jigan gwamnatin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, kuma ma’aikatarsa ce ke jagorantar yaƙi da rashawa a lokacin.
Kotun ba ta sanar da takaimaiman sabuwar ranar da za ta dawo domin yanke hukuncin ba, sai dai ta bayyana cewa za a sanar da lauyoyin ɓangarorin biyu ta hanyar rubutacciyar wasiƙa nan ba da jimawa ba.













