Hukumar Kwastam ta Nijeriya (NCS), ta kama kulli 3,300 na abubuwan fashewa da aka yi yunkurin shigo da su daga Ghana ta hanyar iyakar Seme ba bisa ƙa’ida ba.
Hukumar ta ce baya ga abubuwan fashewar, jami’anta sun kuma kama kayan abinci da lokacin amfaninsu ya shuɗe, miyagun ƙwayoyi, shinkafar ƙasashen waje da sauran kayayyakin da doka ta hana shigowa da su, waɗanda jimillar darajar harajinsu ta kai Naira miliyan 365.16.
Mai Kula da Yankin Kwastam na Seme, Kontrola Abdullahi Shuaibu Kaila, ne ya bayyana hakan ranar Talata a Seme, inda ya kuma bayyana cewa, hukumar ta tara Naira biliyan 19.84 a matsayin kuɗin shiga tsakanin watan Janairu da Yuli na shekarar 2026.
Ya ce adadin ya nuna ƙarin kashi 24.45 cikin ɗari idan aka kwatanta da Naira biliyan 15.94 da hukumar ta tara a dukkan shekarar kasafin kuɗi ta 2025.














