A jiya Talata, mataimakin firaministan kasar Sin Liu Guozhong, ya halarci taron kolin musamman da aka gudanar ta kafar bidiyo, game da yadda kasashen Afirka za su fuskanci annobar cutar Ebola, bisa gayyatar da aka yi masa, inda kuma ya gabatar da jawabi.
Cikin jawabinsa, Liu Guozhong ya ce kasar Sin da kasashen Afirka, suna da makoma ta bai daya, kuma kasar Sin ta riga ta samar da taimakon jin kai cikin gaggawa ga Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo, da kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU. A sa’i daya kuma, ta tura tawagar kwararrun jami’an kiwon lafiya zuwa Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo, inda kwararru a fannin kiwon lafiya kimanin dubu 1 suka hada kai da jama’ar kasashen Afirka wajen yaki da annobar. A nan gaba kuma, kasar Sin za ta aiwatar da matakin hadin gwiwar kiwon lafiya a tsakanin Sin da Afirka, bisa tsarin taron dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka, tare da yin kira ga gamayyar kasa da kasa da su samar da karin goyon baya ga kasashen Afirka.
Shugaban karba-karba na kungiyar AU, kana shugaban kasar Burundi Evariste Ndayishimiye, ya jagoranci taron, inda shugabanni, da manyan jami’ai daga kasashen Afirka sama da 10, kamar Afirka ta Kudu, da Equatorial Guinea, da Zimbabwei da dai sauransu, da wakilan hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, da na wasu kungiyoyin kasa da kasa da na shiyyoyi, da kuma wakilan rukunin kawance da kasashen Afirka daga sauran nahiyoyi suka halarci taron. (Mai Fassara: Maryam Yang)















Discussion about this post