ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikata Sun Buƙaci Ƙara Mafi Ƙarancin Albashi Zuwa Naira 300,000

by Sulaiman
7 days ago
Albashi

Kungiyar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya (FWF) ta rubuta wa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da Majalisar Dokokin Tarayya, tana neman a gaggauta sake duba albashin ma’aikatan gwamnatin tarayya tare da kara mafi karancin albashi daga Naira 70,000 zuwa Naira 300,000.

A cikin wasikar mai kwanan wata 2 ga Satumba, 2026, wadda mai kula da kungiyar ta kasa, Andrew Emelieze, da Babban Sakataren kungiyar, Ogundele Ayodele, suka sanya wa hannu, an bukaci Shugaban Majalisar Dattawa da Kakakin Majalisar Wakilai su ɗauki matakin da ya dace, ta hannun Magatakardar Majalisar Dokokin Tarayya.

Shugaba Tinubu, Alkalin Alkalai na Nijeriya da Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya ma na cikin wadanda aka aikawa wasikar.

ADVERTISEMENT

Kungiyar ta kuma nemi a sanya albashin ma’aikatan da ke mataki na 17 zuwa Naira miliyan 1.5, tana mai cewa tsarin albashin da ake amfani da shi yanzu bai dace da yanayin tattalin arzikin da ma’aikatan gwamnatin tarayya ke fuskanta ba.A cikin wasikar, ma’aikatan sun ce: “Muna kira da a yi adalci tare da gaggauta sake duba albashi yanzu, a kara mafi karancin albashin tarayya zuwa Naira 300,000, sannan a sanya mafi girman albashi na Naira miliyan 1.5 ga ma’aikatan dake mataki na 17.”

FWF ta ce bukatar ta samo asali ne daga abin da ta bayyana a matsayin rashin cikakken aiwatar da sabon mafi karancin albashin Naira 70,000 da aka amince da shi a shekarar 2024.

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

Kungiyar ta yi zargin cewa ma’aikatan gwamnatin tarayya ba su samu cikakken karin albashin da ya kamata ba, biyo bayan karin mafi karancin albashi, da kuma wasu alawus-alawus da ke da alaka da shi.

Ta ce, “Zai ba ku mamaki ku ji cewa Gwamnatin Tarayya ba ta aiwatar da sabon mafi karancin albashin kasa gaba daya ba tun daga watan Yulin 2024. Mun dade muna fafutukar ganin an aiwatar da cikakken karin albashin da ya kamata biyo bayan sabon mafi karancin albashin.”

A cewar ma’aikatan, sake duba tsarin albashin da aka yi a shekarar 2024 ya kara mafi karancin albashi daga Naira 30,000 zuwa Naira 70,000, amma hakan ya haifar da karin Naira 40,000 kacal ga kowane mataki a cikin ma’aikatan gwamnatin tarayya.

Albashi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Next Post
Za’a Dakatar Da Wasa A Farkon Minti 10 Na Kowane Wasa A Kasar Argentina Saboda Girmama Messi

Za'a Dakatar Da Wasa A Farkon Minti 10 Na Kowane Wasa A Kasar Argentina Saboda Girmama Messi

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.