ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatar Tsaro Na Amfani Da Ofishin NSA Wajen Gallaza Wa ’Yan Adawa – Gwamnatin Zamfara

by Sulaiman
6 months ago
NSA

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana matuƙar damuwar ta kan abin da ta kira amfani da ƙarfin Gwamnatin Tarayya wajen gallaza wa da tsoratar da ’yan adawa a jihar, tana mai cewa wannan al’amari na barazana ga dimokuraɗiyya da tsarin doka a Nijeriya.

 

A cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, gwamnatin ta ce ba ta da wani zabi face ta sanar da jama’a yadda Ƙaramin Ministan Tsaro ke amfani da ofishin Mai Ba Shugaban ƙasa Shawara kan Tsaro, wato NSA, wajen gallaza wa ’yan adawa da gwamnati a Zamfara.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Ta Biya ‘Yan Wasan Super Eagles Haƙƙoƙinsu
  • An Kama Mutane 8 Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Ƙunar Baƙin Wake A Masallacin Borno

Sanarwar ta bayyana cewa, gwamnatin ta samu labari mai tayar da hankali dangane da sace Saleem Abubakar, wanda ke aiki a matsayin Mataimaki na Fasaha a Ofishin Gwamnan Jihar Zamfara, inda aka ce an yi garkuwa da shi a birnin Abuja a ranar da ta gabata.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

A cewar gwamnatin, wasu jami’ai na musamman daga ofishin NSA ne suka aikata wannan lamari ba tare da nuna wata takardar kama shi ba.

 

An ce an ɗauki Saleem Abubakar zuwa wani wuri da ba a bayyana ba, sannan aka riƙa ɗaukar sa daga wuri zuwa wuri domin boye sahun takamaiman inda yake.

 

Abin da ya fi tayar da hankali, a cewar sanarwar, shi ne yadda aka danganta wannan lamari kai tsaye da Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, wanda aka ce ya yi amfani da ofishin NSA wajen shirya wannan aiki.

 

Gwamnatin Zamfara ta bayyana hakan a matsayin wani lamari mai hatsari da ya kamata ’yan Nijeriya su yi Alla-wadai da shi baki ɗaya.

 

Sanarwar ta ce, yin amfani da manyan hukumomin tsaro na ƙasa wajen cin zarafin ’yan adawar siyasa abu ne da ke lalata amincewar jama’a ga tsaro, tare da jefa martabar ƙasa cikin haɗari.

 

Ta jaddada cewa babu wata matsala ko sabani da ya isa a tauye ’yancin ɗan ƙasa ko a karya doka ta hanyar sace mutum ba tare da bin hanyoyin shari’a ba.

 

Gwamnatin Zamfara ta yi kira ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya yi gaggawar bibiyar lamarin tare da kiran ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro, tana mai gargaɗin cewa irin waɗannan ayyuka na iya janyo mummunan tasiri ga sunan Nijeriya a idon duniya.

 

Ta kuma ce idan har akwai wata zargi ko matsala da ake dangantawa da Saleem Abubakar, abin da ya dace shi ne a gurfanar da shi a gaban kotu bisa tanadin doka, ba wai a yi garkuwa da shi ko a tsoratar da shi ta hanyar ƙarfin tsaro ba.

 

A ƙarshe, gwamnatin jihar ta bayyana cewa tana sa ido sosai kan wannan lamari, tare da alƙawarin bin sa har ƙarshe domin tabbatar da cewa an yi adalci kuma an kare martabar dimokuraɗiyya da ’yancin ɗan Adam a Nijeriya.

NSA
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Sulaiman
    Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz
  • Sulaiman
    Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Next Post
Kakakin Sin: Sin Da Afirka Sun Zama Abin Koyi Na Sabon Salon Dangantakar Kasa Da Kasa

Kakakin Sin: Sin Da Afirka Sun Zama Abin Koyi Na Sabon Salon Dangantakar Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.