ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatar Tsaro Na Amfani Da Ofishin NSA Wajen Gallaza Wa ’Yan Adawa – Gwamnatin Zamfara

by Sulaiman
5 months ago
NSA

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana matuƙar damuwar ta kan abin da ta kira amfani da ƙarfin Gwamnatin Tarayya wajen gallaza wa da tsoratar da ’yan adawa a jihar, tana mai cewa wannan al’amari na barazana ga dimokuraɗiyya da tsarin doka a Nijeriya.

 

A cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, gwamnatin ta ce ba ta da wani zabi face ta sanar da jama’a yadda Ƙaramin Ministan Tsaro ke amfani da ofishin Mai Ba Shugaban ƙasa Shawara kan Tsaro, wato NSA, wajen gallaza wa ’yan adawa da gwamnati a Zamfara.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Ta Biya ‘Yan Wasan Super Eagles Haƙƙoƙinsu
  • An Kama Mutane 8 Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Ƙunar Baƙin Wake A Masallacin Borno

Sanarwar ta bayyana cewa, gwamnatin ta samu labari mai tayar da hankali dangane da sace Saleem Abubakar, wanda ke aiki a matsayin Mataimaki na Fasaha a Ofishin Gwamnan Jihar Zamfara, inda aka ce an yi garkuwa da shi a birnin Abuja a ranar da ta gabata.

 

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

A cewar gwamnatin, wasu jami’ai na musamman daga ofishin NSA ne suka aikata wannan lamari ba tare da nuna wata takardar kama shi ba.

 

An ce an ɗauki Saleem Abubakar zuwa wani wuri da ba a bayyana ba, sannan aka riƙa ɗaukar sa daga wuri zuwa wuri domin boye sahun takamaiman inda yake.

 

Abin da ya fi tayar da hankali, a cewar sanarwar, shi ne yadda aka danganta wannan lamari kai tsaye da Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, wanda aka ce ya yi amfani da ofishin NSA wajen shirya wannan aiki.

 

Gwamnatin Zamfara ta bayyana hakan a matsayin wani lamari mai hatsari da ya kamata ’yan Nijeriya su yi Alla-wadai da shi baki ɗaya.

 

Sanarwar ta ce, yin amfani da manyan hukumomin tsaro na ƙasa wajen cin zarafin ’yan adawar siyasa abu ne da ke lalata amincewar jama’a ga tsaro, tare da jefa martabar ƙasa cikin haɗari.

 

Ta jaddada cewa babu wata matsala ko sabani da ya isa a tauye ’yancin ɗan ƙasa ko a karya doka ta hanyar sace mutum ba tare da bin hanyoyin shari’a ba.

 

Gwamnatin Zamfara ta yi kira ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya yi gaggawar bibiyar lamarin tare da kiran ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro, tana mai gargaɗin cewa irin waɗannan ayyuka na iya janyo mummunan tasiri ga sunan Nijeriya a idon duniya.

 

Ta kuma ce idan har akwai wata zargi ko matsala da ake dangantawa da Saleem Abubakar, abin da ya dace shi ne a gurfanar da shi a gaban kotu bisa tanadin doka, ba wai a yi garkuwa da shi ko a tsoratar da shi ta hanyar ƙarfin tsaro ba.

 

A ƙarshe, gwamnatin jihar ta bayyana cewa tana sa ido sosai kan wannan lamari, tare da alƙawarin bin sa har ƙarshe domin tabbatar da cewa an yi adalci kuma an kare martabar dimokuraɗiyya da ’yancin ɗan Adam a Nijeriya.

NSA
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Kakakin Sin: Sin Da Afirka Sun Zama Abin Koyi Na Sabon Salon Dangantakar Kasa Da Kasa

Kakakin Sin: Sin Da Afirka Sun Zama Abin Koyi Na Sabon Salon Dangantakar Kasa Da Kasa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.