ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatar Tsaro Na Amfani Da Ofishin NSA Wajen Gallaza Wa ’Yan Adawa – Gwamnatin Zamfara

by Sulaiman
8 months ago
NSA

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana matuƙar damuwar ta kan abin da ta kira amfani da ƙarfin Gwamnatin Tarayya wajen gallaza wa da tsoratar da ’yan adawa a jihar, tana mai cewa wannan al’amari na barazana ga dimokuraɗiyya da tsarin doka a Nijeriya.

 

A cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, gwamnatin ta ce ba ta da wani zabi face ta sanar da jama’a yadda Ƙaramin Ministan Tsaro ke amfani da ofishin Mai Ba Shugaban ƙasa Shawara kan Tsaro, wato NSA, wajen gallaza wa ’yan adawa da gwamnati a Zamfara.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Ta Biya ‘Yan Wasan Super Eagles Haƙƙoƙinsu
  • An Kama Mutane 8 Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Ƙunar Baƙin Wake A Masallacin Borno

Sanarwar ta bayyana cewa, gwamnatin ta samu labari mai tayar da hankali dangane da sace Saleem Abubakar, wanda ke aiki a matsayin Mataimaki na Fasaha a Ofishin Gwamnan Jihar Zamfara, inda aka ce an yi garkuwa da shi a birnin Abuja a ranar da ta gabata.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

A cewar gwamnatin, wasu jami’ai na musamman daga ofishin NSA ne suka aikata wannan lamari ba tare da nuna wata takardar kama shi ba.

 

An ce an ɗauki Saleem Abubakar zuwa wani wuri da ba a bayyana ba, sannan aka riƙa ɗaukar sa daga wuri zuwa wuri domin boye sahun takamaiman inda yake.

 

Abin da ya fi tayar da hankali, a cewar sanarwar, shi ne yadda aka danganta wannan lamari kai tsaye da Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, wanda aka ce ya yi amfani da ofishin NSA wajen shirya wannan aiki.

 

Gwamnatin Zamfara ta bayyana hakan a matsayin wani lamari mai hatsari da ya kamata ’yan Nijeriya su yi Alla-wadai da shi baki ɗaya.

 

Sanarwar ta ce, yin amfani da manyan hukumomin tsaro na ƙasa wajen cin zarafin ’yan adawar siyasa abu ne da ke lalata amincewar jama’a ga tsaro, tare da jefa martabar ƙasa cikin haɗari.

 

Ta jaddada cewa babu wata matsala ko sabani da ya isa a tauye ’yancin ɗan ƙasa ko a karya doka ta hanyar sace mutum ba tare da bin hanyoyin shari’a ba.

 

Gwamnatin Zamfara ta yi kira ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya yi gaggawar bibiyar lamarin tare da kiran ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro, tana mai gargaɗin cewa irin waɗannan ayyuka na iya janyo mummunan tasiri ga sunan Nijeriya a idon duniya.

 

Ta kuma ce idan har akwai wata zargi ko matsala da ake dangantawa da Saleem Abubakar, abin da ya dace shi ne a gurfanar da shi a gaban kotu bisa tanadin doka, ba wai a yi garkuwa da shi ko a tsoratar da shi ta hanyar ƙarfin tsaro ba.

 

A ƙarshe, gwamnatin jihar ta bayyana cewa tana sa ido sosai kan wannan lamari, tare da alƙawarin bin sa har ƙarshe domin tabbatar da cewa an yi adalci kuma an kare martabar dimokuraɗiyya da ’yancin ɗan Adam a Nijeriya.

NSA
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Kakakin Sin: Sin Da Afirka Sun Zama Abin Koyi Na Sabon Salon Dangantakar Kasa Da Kasa

Kakakin Sin: Sin Da Afirka Sun Zama Abin Koyi Na Sabon Salon Dangantakar Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.