Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning, ta yi bayani game da ziyarar aiki da shugaban kasar Xi Jinping zai yi a Koriya ta Arewa.
A cewarta, a lokacin ziyarar, manyan shugabannin jam’iyyun kasashen biyu kuma shugabannin kasashen, za su yi musayar ra’ayoyi kan dangantakar dake tsakanin kasashensu da batutuwan da suka shafi bangarorin biyu.
Kuma za su dauki wannan ziyarar a matsayin wata dama ta bunkasa ci gaban dangantaka da kuma bayar da gudummawa ga zaman lafiya, kwanciyar hankali, ci gaba, da kuma wadata a yankin da ma duniya baki daya.
Mao Ning ta bayyana hakan ne yau Jumma’a, a gun taron manema labarai na yau da kullun.
Bugu da kari, yayin da ake bikin Ranar Muhalli ta Duniya a yau, Mao Ning ta ce kasar Sin za ta ci gaba da ba da fifiko ga samun ci gaba mai kiyaye muhalli, ta hanyar daukar matakai na zahiri don inganta ci gaba mai dorewa a duniya da kuma aiki tare da sauran kasashe don gina duniya mai tsafta da kyau.(Safiyah Ma)















Discussion about this post