Shugaban kasa, Bola Tinubu ya tsoma baki kan rikicin da ya biyo bayan zaben fid da gwani da jam’iyyar APC ta gudanar a fadin kasar nan, tare da alkawarin magance koke-koke da suka taso, musamman a jiharsa ta Legas.
Wani majiya mai tushe daga fadar shugaban kasa, ta ce an fara aiwatar da aikin kuma shugaban kasa da shugabannin jam’iyyar za su duba lamarin.
Haka kuma majiyar ta bayyana cewa Shugaba Tinubu ya umarci ‘yarsa, Hajiya Folashade Tinubu-Ojo, da ta dakatar da shirin zanga-zangar da aka tsara kan sakamakon zabuka a Legas har sai an warware koke-koken da ‘yan takara da masu ruwa da tsaki suka bayyana.
Tinubu-Ojo, a yayin wani taro da shugabannin ‘yan kasuwa da masu ruwa da tsaki a ofishinta a Alausa, makon da ya wuce, ta yi barazanar yin zanga-zanga kan abin da ta bayyana a matsayin rashin daidaito a wajen gudanar da zaben fitar da gwani.
Majiyar fadar shugaban kasa ta ce shugaban kasa bai ji dadin rahotannin da ke nuna cewa wadanda aka dora musu alhakkin gudanar da harkokin jam’iyya a Legas na iya yin abin da ya saba wa ra’ayin mambobin jam’iyya ba.
Majiyar ta kara cewa za a sake duba duk korafe-korafen da suka taso daga zaben fitar da gwani a dukkan fadin kasar nan bayan dawowar shugaban kasa Abuja.
A yayin martani ga tarurrukan da aka yi tsakanin wasu ‘yan takara da aka bayyana da Shugaba Tinubu a lokacin hutun Sallah a Legas, majiyar ta ce bai kamata a fassara irin wadannan haduwa a matsayin tabbacin takararsu ba.
“Duk wadannan tarurrukan an shirya su a matsayin wani bangare na tafiyar shugaban kasa tun kafin a gudanar da zaben fid da gwani. Don haka, ganawa da ‘yan takarar da aka sanar da shugaban kasa ba ya sanya su masu nasara kai tsaye.
“Shugabancin kasa zai duba kiran kuma ya yanke shawara ta karshe. Ba a Jihar Legas kadai ba ne. A duk fadin kasar ne. Wannan shi ya sa tikitin da aka tabbatar kawai har yanzu shi ne na shugaba kasa kadai,” in ji majiyar.















Discussion about this post