Mutane shida, ciki har da mambobi hudu da ke shirin hidimtawa kasa (NYSC), sun kone kurmus a wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da wata motar hilux ta sojoji da kuma motar haya a jihar Adamawa.
Mummunan hatsarin ya faru ne ranar Laraba a yankin Narehi da ke karamar hukumar Girei a kan hanyar Girei zuwa Song, kamar yadda rundunar ’yansandan jihar Adamawa ta bayyana.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, Suleiman Nguroje, ya fitar, ya ce hatsarin ya shafi motar sojoji da ke tafiya daga Gombi zuwa Yola da kuma motar haya kirar Homa dauke da fasinjoji biyar daga Yola zuwa Mubi.
Nguroje ya ce binciken farko ya nuna cewa motocin biyu sun yi karon gaba da gaba ne, lamarin da ya sa motar hayar ta kife tare da kamawa da wuta.
A cewar ’yansanda, bayanan farko sun nuna cewa hudu daga cikin waɗanda suka mutu mambobin NYSC ne da aka tura jihar Adamawa domin yi wa kasa hidima.
An bayyana sunayen biyu daga cikin masu hidimtawa kasar da Suleuman Juliet da Usman Shuaibu, waɗanda duk ’yan asalin jihar Kaduna ne, yayin da ake ci gaba da kokarin gano sauran waɗanda suka mutu.















Discussion about this post