Gwamnatin tarayya ta mayar da hedikwatar gudanarwa ta Hukumar Yaki da Kwararowar Hamada ta Kasa (NAGGW) daga Abuja zuwa jihar Kano a wani mataki na dabaru da nufin karfafa yaki da kwararar hamada, lalacewar kasa da sauyin yanayi a yankin Arewa.
Ministan Muhalli, Balarabe Abbas Lawal, ne ya sanar da matakin, yana mai cewa hakan ya yi daidai da ajandar “Renewed Hope” ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu, kuma an yi shi ne domin kusantar da hukumar ga al’ummomin da matsalolin muhalli suka fi shafa kai tsaye.
Ya ce daga yanzu hukumar za ta gudanar da ayyukanta daga harabar ‘Afforestation Programme Coordinating Unit’ (APCU) da ke Kano, domin inganta sa ido, gudanarwa da aiwatar da ayyuka.
Ministan ya ce, “Mayar da hukumar zuwa Kano zai sanya ta a tsakiyar ayyukanta tare da kusantar da yanke shawara ga jama’a da al’ummomin da matsalar hamada da sauyin yanayi ke shafa kai tsaye.”














Discussion about this post