Yayin da ake kusantar ranar fara aiwatar da manufar kawar da harajin kwastam gaba daya da Sin za ta dauka kan kasashe 53 na nahiyar Afirka da ke da huldar diplomasiyya da ita, kamfanonin Sin da yawa suna kara shiga kasar Zimbabwe domin neman damar hadin gwiwa a fannin kasuwanci.
An gudanar da taron hadin gwiwar gwamnatin Zimbabwe da masu sayen kayayyakin gona na Sin a jiya Laraba a lardin Manicaland na kasar, inda jami’an noma na Zimbabwe, da wakilan manoma, da masu sayen kayayyakin noma na Sin suka cimma yarjejeniyoyin hadin gwiwa da yawa.
A wajen taron, babban jami’in hukumar inganta ciniki ta Zimbabwe ko (ZimTrade) Allan Majuru, ya ce a ‘yan shekarun nan, kayayyakin noma na Zimbabwe kamar avocado, da blueberries, da macadamia nuts da sauransu, sun samu karbuwa sosai a kasuwar Sin saboda ingancinsu. Kuma Zimbabwe tana inganta matakan da suka dace don amfani da manufar kawar da haraji don kara fadada fitar da kayayyakin noma zuwa Sin.
Bangaren Sin zai fara aiwatar da matakin soke harajin kwastam gaba daya ga kasashe 53 na Afirka da ke da alaka da ita, tun daga ranar 1 ga watan Mayu dake tafe, kuma zai ci gaba da inganta sanya hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwar tattalin arziki, tare da ci gaba da fadada shigar da kayayyakin Afirka kasuwannin Sin ta hanyar inganta tsarin “hanyar shigar da kayayyaki maras shinge” da sauransu.(Amina Xu)















Discussion about this post