Wasu da ake zargin ‘yan fashin babur ne sun yanke hannun wani malami mai suna Isah Sallama a wani mummunan hari da suka kai a ƙaramar hukumar Bunkure ta Jihar Kano.
A wata sanarwa da Sakataren wayar da kai na Masarautar Rano, Nasiru Habu Faragai, ya fitar, ya ce lamarin ya faru ne a daren Laraba a kan titin Funkuyi da ke ƙarƙashin gundumar Buran.
- Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceto Rayuka 4, Dukiyar Naira Biliyan 1 A Watan Maris
- Kano Pillars Sun Yi Alƙawarin Sake Zage Damtse Bayan Rashin Nasarar Wasan Bayelsa
Sanarwar ta bayyana cewa wanda abin ya shafa, mazaunin Sarkin Bakar Rano, ya shiga tsakani ne domin ceton wani Malam Sauwanu Hadi, wanda ‘yan fashin ke ƙoƙarin kwace masa babur da wayarsa.
An ce maharan sun fara ƙoƙarin harbe shi da bindiga, amma bindigar ta ki aiki, lamarin da ya sa suka koma amfani da adda inda suka yanke masa hannu, tare da barinsa cikin mawuyacin hali.
An kai rahoton lamarin ga Sarkin Rano, Mai martaba Muhammad Isa Umaru, ta hannun Hakimin Bunkure, Alhaji Aminu Isa Umaru. Sarkin ya bayyana harin a matsayin abin takaici, ya kuma umarci hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike, tare da bayar da tallafin N100,000 domin kula da lafiyar wanda abin ya shafa, yana kira ga shugabannin al’umma da jami’an tsaro su ƙara ƙaimi wajen daƙile ayyukan fashi da sauran laifuka a yankin.















Discussion about this post