A wannan lokaci da muke rayuwa mai cike da sauye-sauye, da rashin tabbas ta fuskar cudanyar sassan kasa da kasa da ma a yanayin tattalin arzikin duniya, turbar da kasar Sin ke bi wajen bunkasa kanta na kara jan hankulan sassan duniya, tare da jinjinawa musamman daga kasashe masu tasowa abokan tafiyar kasar.
Masharhanta da dama na ganin cewa, sakamako mai gamsarwa da Sin ke samu a fannonin raya kai, sun samu ne sakamakon aiki tukuru, da dunkule sassan neman ci gaba, da suka hada da biyayya ga akidun kasa, da daidaita hakan da salon siyasa, inda kasar ke ta kara kaimin bunkasa tattalin arzikinta, da rage fatara tsakanin al’umma, da gina muhimman ababen more rayuwa bisa tsari na dogon lokaci.
Cikin shekaru sama da 40, mun ga yadda kasar Sin ta sauya daga mai dogaro gaba daya ga noma, zuwa kasa ta biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya. Wannan sauyi ya haifar da kubutar miliyoyin al’ummun kasar daga kangin talauci, tare da kafa ginshikin raya masana’antu da samar da ababen more rayuwa mafiya inganci a duniya.
Don haka, muna iya cewa ga dukkanin kasashe masu tasowa dake fama da kalubalen raya masana’antu, da zamanantar da birane, da zamanantar da tattalin arzikinsu, kasar Sin ta riga ta samar da kyakkyawan misali da bai danganci makalewa wata akida daya tilo ba.
Ga kasashe masu tasowa, suna iya koyi da matakan da kasar Sin ta aiwatar, na gudanar da sauye-sauye a cikin gida, da bude kofofinsu ga sassan waje gwargwadon yanayin da suke ciki. Har ila yau suna iya dagewa ga aikin samar da ababen more rayuwa domin hade yankunansu wuri guda. Bugu da kari, su samar da tsare-tsaren neman ci gaba na dogon lokaci. Kazalika, su aiwatar da manufofin yaki da fatara yadda ya kamata, duka daga kyawawan misalai na nasarorin raya kai da tuni kasar Sin ta ci gajiyarsu. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post