Kwanan nan, birnin Xiamen na lardin Fujian dake kudancin kasar Sin ya zama wurin da ’yan kasuwa na duniya ke nuna sha’awar zuwa, domin a nan, ana gudanar da taron tattaunawa kan zuba jari da kasuwanci na sassan kasa da kasa na kasar Sin wato CIFIT karo na 26.
’Yan kasuwa daga kasashe da yankuna 129 suna taron domin neman damar kasuwanci, ciki har da kamfanonin Amurka da dama. Shugabannin wasu kamfanonin kasar da yawa sun ce, Sin ita ce “zabin da suke tsayawa da shi”.
Shugaban kungiyar kasuwanci ta Amurka a Sin, Michael Hart ya ce, “Ita ce shekara ta uku a jere da nake halartar wannan taron zuba jari da kasuwanci. Kowace shekara, tafiyar ba ta zama mara sakamako ba. Wannan kuma shi ne dalilin da ya sa muke zuwa kowace shekara.”
Li Yadan, mataimakiyar shugaban kamfanin Avanci dake kula da harkokin gwamnati a Asiya, ta ce, “A bana, shi ne karo na biyu da muke halartar taron. A ganinmu wannan wani dandali ne mai kyau kwarai. Ta hanyar halartar ayyukan da suka dace, za mu iya sanin manufofin bude kofa na kasar Sin.” (Bilkisu Xin)














