Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning, ta bayyana cewa, Sin da Indiya na shirye-shiryen ganawar shugaba Xi Jinping da firaministan Indiya Narendra Modi, a yayin taron kolin BRICS karo na 18 da za a gudanar a New Delhi.
Mao Ning, ta bayyana cewa kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da Indiya wajen bin jagoranci bisa manyan tsare-tsare na shugabannin biyu, da kallon dangantakar kasashen biyu ta mahangar manyan tsare-tsare kuma cikin dogon zango, da karfafa tuntubar juna, da fadada hadin gwiwa, da warware sabani ta hanyar da ta dace, domin zama abokai makwabtan juna na kwarai kuma masu hadin gwiwa da ke tallafa wa samun nasarar juna.
Kazalika, ta ce kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da dukkan abokan hadin gwiwa na BRICS wajen taimaka wa gagarumin hadin gwiwar BRICS ya ci gaba da bunkasa ba tare da tangarda ba. Mao ta yi wannan bayani ne a wani taron manema labarai na yau da kullum, lokacin da aka tambaye ta game da abubuwan da Sin ke tsammani game da taron kolin BRICS karo na 18.
Shugaban kasar Sin Xi Jinping zai halarci taron kolin da ke tafe kuma ya gabatar da wani muhimmin jawabi, da yin mu’amala sosai da shugabannin wasu kasashe kan manyan batutuwa, ciki har da yanayin da duniya ke ciki a yanzu, da ci gaban tsarin BRICS, da zurfafa hadin gwiwa a aikace, sannan ya gabatar da muhimman shirye-shirye da shawarwarin kasar Sin domin tsara hanyar da za a bi game da bunkasa gagarumin hadin gwiwar BRICKS a matakin koli, kamar yadda ta bayyana. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














