Duk da fara yaƙin neman zaɓe na shugaban ƙasa da majalisar tarayya na zaɓen 2027 bisa ga dokar zaɓe ta 2026, manyan jam’iyyun siyasa har yanzu ba su ƙaddamar da kwamitocin yaƙin neman zaɓensu ba.
Bincike ya nuna cewa bisa ga dokar zaɓe ta 2026, an fara yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa da na majalisar ƙasa tun daga ranar 19 ga Agusta.
Amma makonni biyu bayan wa’aɗin ƙarshe, jam’iyyun siyasa har yanzu sun jinkirta ƙaddamar da kwamitocin yaƙin neman zaɓensu.Ko da yake jam’iyyar APC mai mulki ta sanar da ƙwamitin kamfen na shugaban ƙasa a ranar 22 ga Agusta, sai kuma har yanzu jam’iyyar ba ta ƙaddamar da wannan kwamitin ba.
Amma sakataren a jam’iyyar, Sanata Ajibola Bashiru, ya ce yaƙin neman zaɓe na iya ci gaba ko da an riga an ƙaddamar da kwamitocin kamfen na shugaban ƙasa ko kuma ba a ƙaddamar da su ba, ko da an ƙaddamarwar a hukumance ko a’a.
Sakataren jam’iyyar APC, Sanata Ajibola wanda ya yi magana da manema labarai a ranar Lahadi, ya ce jam’iyyar ta fara kamfen ɗinta, duk da jinkirin da aka samu wajen ƙaddamar da kwamitin yaƙin neman a hukumance.
Lamarin yana kama da haka a jam’iyyar ADC, inda sakataren yaɗa labaran jam’iyyar na ƙasa, Malam Bolaji Abdullahi, ya ce za a ƙaddamar da kwamitin yaƙa neman zaɓer nan ba da jimawa ba.
Shugabannin jam’iyyun da wakilanmu suka yi magana da su a ranar Lahadi sun ce rashin aaddamar da kwamitocin yaƙin neman zaɓen bai kamata a jinkirta shi ba.
APC ta ce ta damuwa game da babbar rashin ƙaddamar da kwamitin yaƙin neman zaɓen a hukumance.Fadar shugaban ƙasa ta fitar da jerin sunayen mambobin kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a ranar 22 ga Agusta, inda Shugaba Bola Tinubu ya zama shugaban tawagar yaƙin neman zaɓensa.
Tsohon gwamnan Jihar Zamfara kuma sanata mai wakiltar Zamfara ta yamma, Abdulaziz Yari, an sanar da shi a matsayin daraktan janar, yayin da gwamnan Jihar Imo, Sanata Hope Uzodinma, aka zaɓe shi a matsayin sakatare.
A yayin yin da yake tattaunawa da manema labarai a wata hira ta wayar tarho, Sanata Bashiru ya bayyana cewa ƙaddamar da kwamitin yaƙi neman zaɓen kawai biki ne, kamar yadda ya lura cewa wasu mambobin kwamitin yaƙin neman zaɓe tun daga baya sun fara yaƙin neman zaɓen ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar.
Haka zalika, jam’iyyar ADC ta ce nan ba da jimawa ba za ta sanar da kwamitin yaƙin neman zaɓentaa da ranar ƙaddamarwa kafin zaɓen 2027.Sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar, Malam Bolaji ya bayyana haka a ranar Lahadi a Abuja yayin da yake zantawa da manema labarai.
Bolaji, yayin da yake amsa tambayoyi kan jinkirin kafa kwamitin, ya ce jam’iyyar ba ta cikin wani matsin lokaci.“Na faɗa cewa ba za a iya magana kan jinkiri ba idan ba ka da wa’adin ƙarshe. Don haka, za mu sanar da kwamitin yaƙin neman zaɓe lokacin da muka shirya kuma mu sanar da ranar ƙaddamarwa. Za mu sanar da shi nan ba da jimawa ba,” in ji shi.
Mai magana da yawun ADC bai bayar da takamaiman ranar sanarwar ba, amma ya ce ana ci gaba da tattaunawa a cikin jam’iyya don tabbatar da cewa kwamitin na nuna tsarin jam’iyyar wajen zaɓen 2027.
A cikin ƴan watannin da suka gabata, jam’iyyar ta kasance tana sake tsara kanta kuma tana jawo sabbin mambobi yayin da harkokin siyasa ke fara samun ƙarfin gaske kafin zaɓen 2027.
Sai dai jam’iyyar Accord na nuna wani yanayi na daban, inda shugabanninta na ƙasa suka ce ba za su kafa kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa ba idan babu wani ɗan takara na shugaban ƙasa da zai ɗaga tutar jam’iyyar.
A kwanan nan an samu takaddama tsakanin shugabancin jam’iyya da ɗan takarar shugaban ƙasa, Dakta Gbenga Olawepo Hashim.
Yayin da yake magana da manema labarai, sakataren yaɗa labarai na ƙasa na jam’iyyar Accord, Joseph Omorogbe, ya ce ya rage ga kwamitin zartarwa na jam’iyyar ta yanke shawarar mataki na gaba yayin da jam’iyyar ke sake haɗewa don wani taron gaggawa na sanar da ƴan Nijeriya wanda zai ɗaga tutar jam’iyyar a zaɓen shugaban ƙasa na shekara mai zuwa.
Kusan makonni uku bayan hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta buɗe ƙofar yaƙin neman zaɓe, wasu jam’iyyun, ciki har da PDP, ba su bayyana tsare-tsaren yaƙin neman zaɓensu ba.Sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar, Honourable Jungudo Haruna Mohammed, ya shaida wa manema labarai cewa PDP za ta yanke shawara kan yadda za ta aiwatar da shi bisa ga natsuwarta ba tare da tilas ta bin wani jam’iyyar siyasa ba.
“PDP ba ta yanke shawara kawai saboda abin da mutane ke tunani ko suka ce. Muna yanke shawara ne lokacin da ya dace mu yi haka, mafi muhimmancin lokacin da ya dace.
“Ba wai yadda muka yi sauri ba ne, amma yadda muka yi da kyau da kuma abin da muka samu,” in ji shi.
A halin yanzu, jam’iyyar APM ta sanar da fara kamfen ɗinta na shugaban ƙasa na 2027, inda ɗan takararta, Gwamnan Jihar Oyo, Injiniya Seyi Makinde, ya ƙaddamar da ofishin kamfen ɗin shugaban ƙasa na jam’iyyar a Abuja a ranar Litinin.
Sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar, Mista Abubakar Yusuf, wanda ya bayyana haka, ya ce ofishin kamfen na shugabancin Makinde da Daura zai zama cibiyar da ke tsara ayyukan kamfen a matakin ƙasa.
Yusuf ya ce yaƙin neman zaɓen zai kasance mai maida hankali kan matsalolin mutane, sannan zai mai mayar da hankali kan zaɓin manufofi mulkin Makinde, wanda yake fafatawa takarar shugaban ƙasa tare da Alhaji Lawan Daura, a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyya.














