A halin yanzu, duniya ta shiga wani sabon zamani mai cike da tashin hankali da sauye-sauyen yanayin al’amura. Fiye da kowane lokaci, an fi bukatar farfado da ra’ayin cudanyar bangarori da dama, da dagewa kan bin doka da oda, da karfafa ingancin jagorantar harkoki. Wannan ya sa darajar zamani da muhimmancin aiwatar da shawarar inganta jagorantar harkokin duniya kara fitowa fili.
A daidai wannan muhimmin lokaci, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kaddamar da shawarar inganta jagorantar harkokin duniya a watan Satumba na 2025, inda ya jaddada muhimman ka’idoji guda biyar da suka hada da daidaiton ikon mulkin kai, da bin dokokin kasa da kasa, da aiwatar da ra’ayin cudanyar bangarori da dama, da sanya moriyar mutane a kan kome, da kuma mayar da hankali kan bukatar daukar takamaiman matakai, wadanda suka samar da dabarar Sin game da babbar tambayar dake gabanmu a wannan zamani, wato “Wane irin tsarin gudanar da harkokin duniya ne ya kamata a gina, kuma ta yaya za a gyara da inganta shi.”
Shawarar ta amsa bukatun bai-daya na kasashe daban daban na kyautata tsarin jagorantar harkokin duniya, da fadada hanyoyin aiwatar da manufar gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga daukacin bil-Adama, sannan ta bude sabon babi a fagen tsarin ilimi mai alaka da siyasar duniya.
Tun bayan kaddamarwar shawarar, ta sami gagarumin goyon baya da karbuwa daga al’ummar duniya.
Fiye da watanni tara ke nan, shawarar inganta jagorantar harkokin duniya ta riga ta rikide daga dabarar Sin zuwa aikace-aikace na kasa da kasa, tana kuma kara nuna tasiri da karfin rayuwa mai girma. (Bilkisu Xin)














Discussion about this post