Kasashen Sin da Tanzania da kuma Zambia sun karrama kwararrun Sinawa wadanda suka sadaukar da rayukansu yayin gina layin dogo na Tanzania zuwa Zambia (TAZARA), inda suka yi bikin cika shekaru 50 da fara ayyukan kasuwanci na layin dogon tare da sake jaddada jajircewarsu wajen farfado da shi.
An gudanar da bikin sanya furanni a makabartar kwararrun Sinawan da ke birnin Dar es Salaam, inda kimanin mutane 100 suka fito duk da yayyafin ruwa da aka yi da safiya domin girmama injiniyoyi, masu ayyukan kere-kere, da sauran ma’aikata Sinawa su 70 wadanda suka rasa rayukansu yayin gina layin dogon da ya hade Tanzania da Zambia, wanda yake taimaka wa bunkasar Afirka.
Jakadar Sin a Tanzania, Chen Mingjian, ta bayyana cewa ma’aikata sama da 50,000 na kasar Sin sun shiga sahun takwarorinsu na Tanzania da Zambia wajen gina layin dogon, wanda aka fi sani da “Layin jirgin kasa na Uhuru” da “Layin jirgin kasa na Urafiki,” inda suka shawo kan manyan kalubale ta hanyar hadin kai da kuma abota.
A nasa bangare, jakadan Zambia a kasar Tanzania, Mathews Jere ya bayyana layin dogo na TAZARA a matsayin tambarin kyakkyawan fata wanda ya samar wa Zambia da ke cikin kurya wata muhimmiyar hanyar shiga teku, da kuma nuna kudurin ci gaba na shugabannin da suka kafa kasar Julius Nyerere da Kenneth Kaunda.
Kazalika, Lu Haiqiang, manajan daraktan kamfanin gine-gine na kasar Sin da ke shiyyar gabashin Afirka, ya yi karin haske game da kokarin da ake yi na zamanantar da layin dogon bayan wani hadin gwiwa da aka yi na farfado da shi, da kuma bude sabbin damammaki na ci gaban tattalin arziki da ke kan layin, inda ya kara da cewa aikin farfado da layin dogon yana ci gaba da tafiya ba tare da tangarda ba. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














