Kasar Sin ta yi kira ga Amurka da Iran, da su aiwatar da cikakkiyar takardar bayanin fahimtar juna da aka cimma, su kuma warware sabani ta hanyar tattaunawa da shawarwari, kana su kauracewa amfani da karfi.
Da ta bayyana kiran na Sin a yau Laraba, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Mao Ning, ta ce sake barkewar rikici ba zai cika burin ko wanne bangare ba, kuma matakan soji ba za su warware muhimman batutuwan da ake fuskanta ba.
Mao, ta yi tsokacin ne yayin da take amsa tambayoyin ‘yan jarida, game da sake barkewar yanayin tashin hankali na baya-bayan nan a yankin Gabas ta Tsakiya, a taron manema labarai na yau da kullum da aka saba gudanarwa. (Saminu Alhassan)
ADVERTISEMENT
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/













