Wata Kotun Majistare da ke Katsina ta bayar da umarnin tsare Dokta Bashir Kurfi, malami a Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zariy, bisa zargin cewa ya yi wa gwamnatin Jihar Katsina ƙaryar ɗaukar nauyin aikin Hajjin wasu shugabannin ’yan bindiga.
An gurfanar da Dokta Kurfi a gaban kotu ne kan zargin ɓata suna da kuma yaɗa bayanan ƙarya, bayan wasu kalaman da ake zargin ya yi a wata hira da gidan talabijin ɗin Trust TV.
Masu gabatar da ƙara sun shaida wa kotu cewa kalaman nasa ƙarya ne kuma za su iya ɓata sunan gwamnatin Jihar Katsina.
Don haka suka nemi a ci gaba da tsare shi yayin da ake gudanar da bincike.
Sai dai lauyan Dokta Kurfi ya roƙi kotu ta bayar da belinsa, yana mai cewa ya kamata a bar shi ya fuskanci shari’ar cikin ’yanci.
Alƙalin Kotun Majistaren, ya amince da buƙatar masu gabatar da ƙara, inda ya umarci a ci gaba da tsare malamin a sashen binciken manyan laifuka (SCID) na rundunar ’yansandan Jihar Katsina.
Dokta Kurfi ya musanta zargin da ake masa, inda ya ce ba shi da laifi.
Kotun ta ɗage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 14 ga watan Yuli, 2026.













