Ministan kiwon lafiya na jamhuriyyar demokradiyar Kongo (DRC), Samuel Roger Kamba Mulamba, ya gana da jakadan Sin dake DRC, Zhao Bin, da ma tawagar kwararrun likitoci da Sin ta tura zuwa kasar don tallafa wa shawo kan yaduwar cutar Ebola a birnin Kinshasa, babban birnin kasar jiya Talata.
Yayin ganawar, mista Kamba ya bayyana godiya ga gwamnatin Sin bisa tura tawagar kwararrun likitoci zuwa kasar domin tallafa wa shawo kan yaduwar cutar Ebola a lokaci mafi muhimmanci wajen kandagarki da dakile cutar Ebola. Sin ta dade tana goyon bayan bangaren DRC wajen fuskantar kalubalen kiwon lafiyar jama’a, kuma bangarorin biyu a ko da yaushe suna “haye siradi tare.”
A nasa bangare, jakada Zhao Bin ya bayyana cewa, cutar Ebola ba ma kawai tana haifar da koma-baya ga kiwon lafiyar jama’ar DRC kawai ba, har ma tana kawo barazana ga kiwon lafiyar jama’a na yankin da ma dukkan kasashen duniya. Bangaren Sin ya dade yana kira da a gina tsarin kiwon lafiya mai makoma ta bai daya ga daukacin bil-adama, kuma yana fatan ci gaba da ba da tallafi ga bangaren DRC bisa yanayin yaduwar cutar da bukatu na zahiri na DRC.
Wani rahoton da ofishin kula da harkokin yankin Afirka na kungiyar WHO ya fitar jiya Talata ya nuna cewa, cutar Ebola a DRC na ci gaba da ta’azzara, inda adadin wadanda suka mutu sakamakon cutar ya zarce 520, kuma har yanzu ba a shawo kan yaduwar cutar a yankin gabashin kasar da ya fi fama da cutar ba.(Safiyah Ma)














