An tabbatar da mutuwar mutane huɗu bayan wata motar Golf Wagon ta faɗa cikin madatsar ruwan (Dam) Tomar da ke ƙaramar hukumar Danbatta a Jihar Kano a yammacin ranar Talata.
Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ce ta bayyana hakan cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, ACFO Saminu Abdullahi, ya fitar a ranar Laraba.
A cewar sanarwar, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7:10 na yamma lokacin da sashen kashe gobara na Danbatta ya samu kiran gaggawa daga wani mazaunin yankin mai suna Suleman.
Abdullahi ya ce motar, wadda ba a san lambar rajistarta ba, na kan hanyarta daga Kano zuwa Roni a Jihar Jigawa lokacin da ta afka cikin madatsar ruwan.
Sanarwar ta ƙara da cewa mutane 10 ne ke cikin motar lokacin hatsarin.
“Jami’an kashe gobara daga ofishin Danbatta sun garzaya wurin da lamarin ya faru tare da samun nasarar ceto dukkan waɗanda abin ya shafa,” in ji sanarwar.















Discussion about this post